Ma’aikatar harkokin cikin gida ta Saudiyya ta yi gargaɗin cewa, za a ci tarar waɗanda su ke saɓawa dokokin da a ka saka na yaƙi da annobar korona.
Jaridar Saudi Gazette ta rawaito cewa, ma’aikatar ta ce ƙin saka takunkumi ko ƙyalle, domin rufe baki da hanci babban laifi ne wanda zai iya jazawa mutum ya biya tarar riyal 1000.
Ma’aikatar ta bayyana cewa, za a ci gaba da ruɓanya kuɗin idan mutum ya ci gaba da saɓawa dokar, har kuɗin su kai riyal dubu 100.
Tun daga Alhamis ɗin da ta gabata ne dai kasar Saudiyya ta kara saka dokokin kiyaye yaɗuwar korona, kamar saka takunkumi da bayar da tazara a daidai lokacin da a ke cikin fargabar yaɗuwar sabon nau’in korona na Omicron.