fidelitybank

Idan ba a dauki mataki a kan kisan Hanifa ba zamu shige gaba – Human Right

Date:

Kungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Global Community for Human Right Network, ta ce matuƙar ba a ɗauki matakin da ya dace akan Abdulmalik Muhammad Tanko da ake zargi da kashe Hanifa Abubakar, za su shige gaba domin yin abinda ya dace.
Jami’in hulɗa da jama’a na kungiyar, Muhammad A-A King, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da ya fitar mai ɗauke dasa hannunsa aka rabawa manema labarai a rana Asabar.
Ya ce “Munsan dukkanin irin abubuwan da suke faruwa a ƙasar nan na ƙarancin ɗaukar mataki akan al’amarin makamancin na Hanifa da ya faru, domin haka muke kira da kakkausar murya da a ɗauki matakin da ya dace akan kisan Hanifa Abubakar ko kuma mu wuce gaba har muga an ɗauki matakin da ya dace,” in ji A-A King.
Hakazalika Shugaban Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam, Ambasada Karibu Yahya Lawan Kabara, ya ce, matuƙar jami’an tsaro da ma’aikan shari’a harma da ɓangaren gwamnatin Kano ba su ɗauki matakin da ya dace ba, babu shakka za su ɗauki matakin doka a duk ɓangaren da aka samu sakaci.

naija hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp