Kungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Global Community for Human Right Network, ta ce matuƙar ba a ɗauki matakin da ya dace akan Abdulmalik Muhammad Tanko da ake zargi da kashe Hanifa Abubakar, za su shige gaba domin yin abinda ya dace.
Jami’in hulɗa da jama’a na kungiyar, Muhammad A-A King, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da ya fitar mai ɗauke dasa hannunsa aka rabawa manema labarai a rana Asabar.
Ya ce “Munsan dukkanin irin abubuwan da suke faruwa a ƙasar nan na ƙarancin ɗaukar mataki akan al’amarin makamancin na Hanifa da ya faru, domin haka muke kira da kakkausar murya da a ɗauki matakin da ya dace akan kisan Hanifa Abubakar ko kuma mu wuce gaba har muga an ɗauki matakin da ya dace,” in ji A-A King.
Hakazalika Shugaban Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam, Ambasada Karibu Yahya Lawan Kabara, ya ce, matuƙar jami’an tsaro da ma’aikan shari’a harma da ɓangaren gwamnatin Kano ba su ɗauki matakin da ya dace ba, babu shakka za su ɗauki matakin doka a duk ɓangaren da aka samu sakaci.