fidelitybank

Idan ba a dauki mataki a kan kisan Hanifa ba zamu shige gaba – Human Right

Date:

Kungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Global Community for Human Right Network, ta ce matuƙar ba a ɗauki matakin da ya dace akan Abdulmalik Muhammad Tanko da ake zargi da kashe Hanifa Abubakar, za su shige gaba domin yin abinda ya dace.
Jami’in hulɗa da jama’a na kungiyar, Muhammad A-A King, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da ya fitar mai ɗauke dasa hannunsa aka rabawa manema labarai a rana Asabar.
Ya ce “Munsan dukkanin irin abubuwan da suke faruwa a ƙasar nan na ƙarancin ɗaukar mataki akan al’amarin makamancin na Hanifa da ya faru, domin haka muke kira da kakkausar murya da a ɗauki matakin da ya dace akan kisan Hanifa Abubakar ko kuma mu wuce gaba har muga an ɗauki matakin da ya dace,” in ji A-A King.
Hakazalika Shugaban Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam, Ambasada Karibu Yahya Lawan Kabara, ya ce, matuƙar jami’an tsaro da ma’aikan shari’a harma da ɓangaren gwamnatin Kano ba su ɗauki matakin da ya dace ba, babu shakka za su ɗauki matakin doka a duk ɓangaren da aka samu sakaci.

daily 
post news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp