Hukumar tattara haraji ta jihar Kano, (KIRS) ta rabawa ma’aikatanta takardar tuhuma sama da mutane 200.
Shugaban hukumar, Abdurrazak Datti Salihi ne ya bayar da wannan takardar tuhumar tun a ranar jumaa da ta gabata, ya yin rangadi da ya yi a ofishin hukumar da misalin karfe 5:20 na yammacin Juma ar.
Takardar da shugaban ya bayar ga ma’aikatan, ta kunshi bayani kamar haka. An lura cewa ba ka kan kujera a lokacin da shugaban hukumar ya kawo maka ziyara a ofishin ka a ranar Juma’a, 17 ga Disamba, 2021
Bisa la’akari da abubuwan da ke sama, ya kamata ku bayyana dalilin da ya sa baka nan, domin za a dau matakin ladabtarwa a kanka.
Wasu daga cikin ma’aikatan sun bayyana cewar ranar Litinin da Juma a shugaban ya yi rangadi bayan karfe 5 na yamma lokacin wasu sun tashi wasu kuma suna wajen aiki a waje domin duba da cewar aikin na su yawanci ba na zama bane su na yawace-yawace wajen tattara kudaden haraji, Iokacin da ya zo ba mitune shi ne ya dauki sunayen wadanda su ke nan daga bisani wadanda bai same su ba a ka bisu da takardar tuhuma (Query) su sama da dari 200.