fidelitybank

Hukumar samar da aiki ta kasa ta horas da matasa 50 a Kano

Date:

Hukumar samar da aikin yi ta kasa (NDE) ta fara aiwatar da wani horo na kwanaki biyar ga matasa da mata 50 da ba su da aikin yi a Kano a kan aikin noma.

Da yake jawabi a wajen bikin kaddamarwar ranar Litinin a Kano, Kodinetan NDE na jihar, Malam Idris Sani Yakasai, ya ce, makasudin gudanar da horon shi ne samar da ayyukan yi ga matasa.

Ya kara da cewa hakan zai taimaka “Domin inganta hanyoyin noma da ke da alaka da ayyukan noman gargajiya da kuma kara samar da abinci a jihar da kuma tarayya.”

Ko’odinetan ya ce, horon ya kuma yi da nufin rage ci rani zuwa wasu garuruwan da matasa ke yi.

Ya kara da cewa, NDE na da niyyar ba su wasu rancen kudade domin sayen injuna, wanda zai ba su damar shiga cikin karkara.

Yakasai ya ce,”Wadanda aka horas din kuma za a dauki su a matsayin masu sana’o’in dogaro da kai, domin za su iya karban wasu kudade ga manoman don ayyukan”. In ji Yakasai.

Saifullahi Sulaiman, daya daga cikin mahalarta taron, ya godewa gwamnatin tarayya bisa irin wannan horon, sannan ya yi alkawarin aiwatar da abin da suka koya a karshen kwas din.

Sai dai ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta kara yawan wadanda za su halarci horon na gaba, ya kuma bukaci gwamnatin jihar ta yi hakan, domin kara samar da ayyukan yi.

Shi ma Abdul-Rasheed Mohammed, wani mahalarci, ya yaba da wannan karimcin, ya na mai cewa, “Horon ya dace da ni don dogaro da kai da kuma samar da aikin yi.”

www.nigerianews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp