Hukumar samar da aikin yi ta kasa (NDE) ta fara aiwatar da wani horo na kwanaki biyar ga matasa da mata 50 da ba su da aikin yi a Kano a kan aikin noma.
Da yake jawabi a wajen bikin kaddamarwar ranar Litinin a Kano, Kodinetan NDE na jihar, Malam Idris Sani Yakasai, ya ce, makasudin gudanar da horon shi ne samar da ayyukan yi ga matasa.
Ya kara da cewa hakan zai taimaka “Domin inganta hanyoyin noma da ke da alaka da ayyukan noman gargajiya da kuma kara samar da abinci a jihar da kuma tarayya.”
Ko’odinetan ya ce, horon ya kuma yi da nufin rage ci rani zuwa wasu garuruwan da matasa ke yi.
Ya kara da cewa, NDE na da niyyar ba su wasu rancen kudade domin sayen injuna, wanda zai ba su damar shiga cikin karkara.
Yakasai ya ce,”Wadanda aka horas din kuma za a dauki su a matsayin masu sana’o’in dogaro da kai, domin za su iya karban wasu kudade ga manoman don ayyukan”. In ji Yakasai.
Saifullahi Sulaiman, daya daga cikin mahalarta taron, ya godewa gwamnatin tarayya bisa irin wannan horon, sannan ya yi alkawarin aiwatar da abin da suka koya a karshen kwas din.
Sai dai ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta kara yawan wadanda za su halarci horon na gaba, ya kuma bukaci gwamnatin jihar ta yi hakan, domin kara samar da ayyukan yi.
Shi ma Abdul-Rasheed Mohammed, wani mahalarci, ya yaba da wannan karimcin, ya na mai cewa, “Horon ya dace da ni don dogaro da kai da kuma samar da aikin yi.”