fidelitybank

Hukumar samar da aiki ta kasa ta horas da matasa 50 a Kano

Date:

Hukumar samar da aikin yi ta kasa (NDE) ta fara aiwatar da wani horo na kwanaki biyar ga matasa da mata 50 da ba su da aikin yi a Kano a kan aikin noma.

Da yake jawabi a wajen bikin kaddamarwar ranar Litinin a Kano, Kodinetan NDE na jihar, Malam Idris Sani Yakasai, ya ce, makasudin gudanar da horon shi ne samar da ayyukan yi ga matasa.

Ya kara da cewa hakan zai taimaka “Domin inganta hanyoyin noma da ke da alaka da ayyukan noman gargajiya da kuma kara samar da abinci a jihar da kuma tarayya.”

Ko’odinetan ya ce, horon ya kuma yi da nufin rage ci rani zuwa wasu garuruwan da matasa ke yi.

Ya kara da cewa, NDE na da niyyar ba su wasu rancen kudade domin sayen injuna, wanda zai ba su damar shiga cikin karkara.

Yakasai ya ce,”Wadanda aka horas din kuma za a dauki su a matsayin masu sana’o’in dogaro da kai, domin za su iya karban wasu kudade ga manoman don ayyukan”. In ji Yakasai.

Saifullahi Sulaiman, daya daga cikin mahalarta taron, ya godewa gwamnatin tarayya bisa irin wannan horon, sannan ya yi alkawarin aiwatar da abin da suka koya a karshen kwas din.

Sai dai ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta kara yawan wadanda za su halarci horon na gaba, ya kuma bukaci gwamnatin jihar ta yi hakan, domin kara samar da ayyukan yi.

Shi ma Abdul-Rasheed Mohammed, wani mahalarci, ya yaba da wannan karimcin, ya na mai cewa, “Horon ya dace da ni don dogaro da kai da kuma samar da aikin yi.”

general news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp