fidelitybank

Harin Sokoto: Gwamnati na bukatar goyon bayan ‘yan Najeriya – Buhari

Date:

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayyana bakin cikinsa a kan harin da aka kai wa wasu matafiya da ba su ji ba, ba su gani ba a jihar Sokoto.

Sanarwar da fadar shugaban ta fitar a ranar Laraba na cewa, Muhammadu Buhari ya damu matuka da yadda waɗannan ƴan kasa da ba su ji ba, ba su gani ba suka gamu da ajalinsu a kan hanyarsu ta neman halal.

Akalla mutum 21 ƴan bindiga suka ƙona a wata motar fasinja lokacin da su ka yi musu kwanton-bauna a ranar Talata. A cewar BBC.

Sai dai wasu ‘yan uwan fasinjojin sun ce mutanen da ‘yan bindigar suka kona sun kai mutum 42.

Rahotannin sun ce fasinjojin sun fito ne daga karamar hukumar Sabon Birni da ke jihar, domin yin ƙaura zuwa wasu yankunan Najeriya, saboda ta’azzarar hare-haren ‘yan bindiga a inda suke.

Buhari ya jajantawa iyalan waɗanda aka kashe tare da cewa jami’an tsaro za su ci gaba da koƙari na kawo ƙarshen waɗannan miyagun mutane.

Ya ce wannan mummunan al’amari da gwamnatinsa ke fuskanta na buƙatar goyon bayan dukkanin ƴan Najeriya.

daily post nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mu na aiki tuƙuru wajen daƙile ayyukan ta’adda a Najeriya – Christopher Musa

Babban hafsan tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa, ya tabbatarwa...

Mayaƙan ISWAP sun harbe Manoma 23 a Borno

Rahotanni sun bayyana cewa ƙungiyar mayaƙan ISWAP ta kashe...

Real Madrid ta ɗauki ɗan wasan baya daga Bournemouth

Real Madrid ta sanar da sayen ɗan wasan baya...

Gwamnatin Kano ta haramta yin bikin Ƙauyawa da gidajen biki

Hukumar tace fina-finai a jihar Kano ta sanar da...

An kashe ƴan Boko Haram biyar a Borno

Dakarun sojin Najeriya haɗe da wasu maharba sun daƙile...

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta...

An kashe mutane 10 a wani sabon rikici da ya ɓarke a Filato

Aƙalla mutabe 10 ne aka kashe tare da sace...

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta...

Hauhawar farashi ya ragu da kaso 23.71 a Najeriya – NBS

An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga...

Fiye da mutane 100 Makiyaya aka kashe a Jos

An ruwaito cewa an kashe wani makiyayi guda da...

Tinubu ka kori shugaban JAMB – Sowore

Dan siyasa mai fafutuka, Omoyele Sowore, ya yi kira...

Majalisa ta yi watsi da ƙudirin karɓa-karɓa

Majalisar wakilai ta yi watsi da wani ƙudirin doka...
X whatsapp