Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayyana bakin cikinsa a kan harin da aka kai wa wasu matafiya da ba su ji ba, ba su gani ba a jihar Sokoto.
Sanarwar da fadar shugaban ta fitar a ranar Laraba na cewa, Muhammadu Buhari ya damu matuka da yadda waɗannan ƴan kasa da ba su ji ba, ba su gani ba suka gamu da ajalinsu a kan hanyarsu ta neman halal.
Akalla mutum 21 ƴan bindiga suka ƙona a wata motar fasinja lokacin da su ka yi musu kwanton-bauna a ranar Talata. A cewar BBC.
Sai dai wasu ‘yan uwan fasinjojin sun ce mutanen da ‘yan bindigar suka kona sun kai mutum 42.
Rahotannin sun ce fasinjojin sun fito ne daga karamar hukumar Sabon Birni da ke jihar, domin yin ƙaura zuwa wasu yankunan Najeriya, saboda ta’azzarar hare-haren ‘yan bindiga a inda suke.
Buhari ya jajantawa iyalan waɗanda aka kashe tare da cewa jami’an tsaro za su ci gaba da koƙari na kawo ƙarshen waɗannan miyagun mutane.
Ya ce wannan mummunan al’amari da gwamnatinsa ke fuskanta na buƙatar goyon bayan dukkanin ƴan Najeriya.