fidelitybank

Harin Sokoto: Gwamnati na bukatar goyon bayan ‘yan Najeriya – Buhari

Date:

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayyana bakin cikinsa a kan harin da aka kai wa wasu matafiya da ba su ji ba, ba su gani ba a jihar Sokoto.

Sanarwar da fadar shugaban ta fitar a ranar Laraba na cewa, Muhammadu Buhari ya damu matuka da yadda waɗannan ƴan kasa da ba su ji ba, ba su gani ba suka gamu da ajalinsu a kan hanyarsu ta neman halal.

Akalla mutum 21 ƴan bindiga suka ƙona a wata motar fasinja lokacin da su ka yi musu kwanton-bauna a ranar Talata. A cewar BBC.

Sai dai wasu ‘yan uwan fasinjojin sun ce mutanen da ‘yan bindigar suka kona sun kai mutum 42.

Rahotannin sun ce fasinjojin sun fito ne daga karamar hukumar Sabon Birni da ke jihar, domin yin ƙaura zuwa wasu yankunan Najeriya, saboda ta’azzarar hare-haren ‘yan bindiga a inda suke.

Buhari ya jajantawa iyalan waɗanda aka kashe tare da cewa jami’an tsaro za su ci gaba da koƙari na kawo ƙarshen waɗannan miyagun mutane.

Ya ce wannan mummunan al’amari da gwamnatinsa ke fuskanta na buƙatar goyon bayan dukkanin ƴan Najeriya.

nigeria news today 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...
X whatsapp