Gwamnatin jihar Zamfara ta bayyana cewa, har yanzu ba ta karbi tirelolin shinkafa guda 20 da gwamnatin tarayya ta ware ba.
Babban Daraktan yada labarai da sadarwa na Gwamnan Jihar Kwamared Nuhu Salisu Anka ne ya bayyana hakan a wata tattaunawa da manema labarai ta wayar tarho a Gusau babban birnin jihar a ranar Asabar.
A cewarsa, tun da farko gwamnatin tarayya ta sanar da tura kayayyakin ga gwamnatocin jihohi.
Ya kara da cewa, “har yanzu jihar Zamfara ba ta samu rabon ta na tireloli 20 na shinkafa ba, wanda gwamnatin tarayya ta amince da su.
Ya bayyana cewa da zarar kayan sun iso zai tabbatar da an sanar da ‘yan jarida isowar kason na jihar Zamfara.