Mahukuntan kasar Sin na ci gaba da zuba jarinta na malala layin dogo wanda ya taso tun daga Serbia har Arewacin Macedonia ya kuma shiga ta kasar Girka Port of Piraeus.
A wani bincike da aka gudanar a yankin Turai cewa matafiya kan gudanar da zirga-zirgarsu ta kan layin dogo a fanin yankin baki daya maimakon hanyar mota.
Har yanzu dai aikin na ci gaba da gudana na layin dogon, sai dai kuma kungiyar tarayyar turai ta EU ta damu matuka gaya, akan yadda kasar Sin ke ci gaba da mamaye yankin, wanda hakan kungiyar ta ce babbar matsala ne ga tattalin arzikin kasar ta.
Duk da cewa kungiyar tarayyar Turai ta EU, ta bayyana shekarar 2021 a matsayin shekarar layin dogo domin hada dukannin kasashen yankin wuri guda a harkokin zirga-zirga wajen zuba hannun jarint, amma kuma har yanzu hankalinta yafi karkata kan shimfida tituna a kan layin dogon.
Tun dai a ranar 25 ga watan Nuwambar 2015 ne wani jirgin kasa mai gudun kilomita 400 a cikin awa guda ya fara gudanar da jigilarsa tun daga birnin Suzhou ya dangana zuwa Shanhanghai. Wanda Firem minisatan kasar Sin Li Keqiang da shugaban kasar Serbia Aleksandae vucic da kuma shugaban kasar Hungary Viktor Orban suka gana a wani zaman teburi da suka yi a kan gudanar da aikin layin dogon.