fidelitybank

Hamas ta saki Mata uku ƴan Isra’ila

Date:

Hamas ta saki wasu mata uku daga cikin ‘yan Isra’ila da ta yi garkuwa da su tsawon wata goma sha biyar, inda ta danƙa su a hannun ƙungiyar agaji ta duniya ta Red Cross.

‘Yan Isra’ila da dama a birnin Tel Aviv na kasar sun yi ta shewa da murnar sakin nasu da suka kalla a labarai a wani katon allon talabijin da aka girke a birnin. In ji BBC.

Sakin nasu ya kasance ne a wani mataki na aiwatar da yarjejeniyar dakatar da buɗe wuta a tsakanin Hamas da Isra’ila, wadda aka daɗe ana fatan gani.

Matasan matan uku su ne – Doron Steinbrecher, da Romi Gonen da kuma Emily Damari.

Ita ma Hamas ta ce Isra’ila za ta saka mata da sakin aƙalla fursunoni Falasɗinawa 90 a yau, yawanci mata da matasa.

A nan gaba ne kuma Hamas ɗin za ta sake sakin wasu ƙarin ‘yan Isra’ilan talatin amma a rukuni-rukuni a tsawon mako shida.

‘Yan sa’o’i kafin fara aiwatar da yarjejeniyar dakatar da buɗe wutar, hukumar kai ɗauki da Hamas ke tafiyarwa a Gaza ta ce Isra’ila ta kashe aƙalla Falasɗinawa 19 a sababbin hare-hare da ta kai Gaza ta sama.

besda

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mu na aiki tuƙuru wajen daƙile ayyukan ta’adda a Najeriya – Christopher Musa

Babban hafsan tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa, ya tabbatarwa...

Mayaƙan ISWAP sun harbe Manoma 23 a Borno

Rahotanni sun bayyana cewa ƙungiyar mayaƙan ISWAP ta kashe...

Real Madrid ta ɗauki ɗan wasan baya daga Bournemouth

Real Madrid ta sanar da sayen ɗan wasan baya...

Gwamnatin Kano ta haramta yin bikin Ƙauyawa da gidajen biki

Hukumar tace fina-finai a jihar Kano ta sanar da...

An kashe ƴan Boko Haram biyar a Borno

Dakarun sojin Najeriya haɗe da wasu maharba sun daƙile...

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta...

An kashe mutane 10 a wani sabon rikici da ya ɓarke a Filato

Aƙalla mutabe 10 ne aka kashe tare da sace...

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta...

Hauhawar farashi ya ragu da kaso 23.71 a Najeriya – NBS

An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga...

Fiye da mutane 100 Makiyaya aka kashe a Jos

An ruwaito cewa an kashe wani makiyayi guda da...

Tinubu ka kori shugaban JAMB – Sowore

Dan siyasa mai fafutuka, Omoyele Sowore, ya yi kira...

Majalisa ta yi watsi da ƙudirin karɓa-karɓa

Majalisar wakilai ta yi watsi da wani ƙudirin doka...
X whatsapp