Hamas ta saki wasu mata uku daga cikin ‘yan Isra’ila da ta yi garkuwa da su tsawon wata goma sha biyar, inda ta danƙa su a hannun ƙungiyar agaji ta duniya ta Red Cross.
‘Yan Isra’ila da dama a birnin Tel Aviv na kasar sun yi ta shewa da murnar sakin nasu da suka kalla a labarai a wani katon allon talabijin da aka girke a birnin. In ji BBC.
Sakin nasu ya kasance ne a wani mataki na aiwatar da yarjejeniyar dakatar da buɗe wuta a tsakanin Hamas da Isra’ila, wadda aka daɗe ana fatan gani.
Matasan matan uku su ne – Doron Steinbrecher, da Romi Gonen da kuma Emily Damari.
Ita ma Hamas ta ce Isra’ila za ta saka mata da sakin aƙalla fursunoni Falasɗinawa 90 a yau, yawanci mata da matasa.
A nan gaba ne kuma Hamas ɗin za ta sake sakin wasu ƙarin ‘yan Isra’ilan talatin amma a rukuni-rukuni a tsawon mako shida.
‘Yan sa’o’i kafin fara aiwatar da yarjejeniyar dakatar da buɗe wutar, hukumar kai ɗauki da Hamas ke tafiyarwa a Gaza ta ce Isra’ila ta kashe aƙalla Falasɗinawa 19 a sababbin hare-hare da ta kai Gaza ta sama.