fidelitybank

Hajjin 2022: Wani mazaunin England ya fara tattaki zuwa Makka

Date:

 

 

Wani haifaffen England, Adam Muhammed, wanda ya fara tattaki a watan Agustan 2021 zuwa aMakka, Saudi Arebiya domin yin aikin Hajji daga Ingila da kafarsa, ya isa yankin Silivri na arewa maso yammacin Turkiyya.

Muhammad ya fara bulaguro ɗin ne, wacce ya yi wa laƙabi da “Tafiya mai aminci”, ya samu taimakon wasu direbobi a kan hanya, inda har ya samu wani kare da ke shawagi kuma tuni su ka zama abokai ya kuma zame masa ɗan rakiya a kasar Sabiya.

Baturen dan asalin kasar Iraqi ya tashi daga Ingila a watan Agustan 2021 zuwa Makka da kafa, balaguron da ya fara da nufin “fito da dukkan munanan abubuwa.”

Muhammad, wanda ke tare da mafaɗacin abokinsa ya ɗaura niyyar isa Saudiyya a lokacin aikin hajji inda ya wuce kasar Siriya sannan ya wuce kasar Jordan kwanaki 35 da wuce Turkiyya.

Yayin da yake zantawa da Kamfanin Dillancin Labarai na Anadolu (AA) game da tafiyar tasa zuwa kasa mai tsarki, Muhammed dan kasar Iraqi da ya kwashe shekaru 25 yana zaune a Ingila ya ce: “Na fara tafiya ne a ranar 1 ga watan Agustan bara. Ina fatan zan yi shi cikin lokaci don aikin hajji na gaba.

“Ina fatan duk tafiyar a kafa ce. Akwai wata murya mai karfi a cikina tana cewa zan iya zuwa Makka ta hanyar tafiya daga gidana. Ba zan iya yin watsi da wannan muryar ba. Yana cikin cikina kamar dutsen mai aman wuta,” in ji shi.

Mohammed ya kara da cewa ya shirya tafiyar tsawon wata biyu kuma wata kungiyar Birtaniya ce ta taimaka masa.

Mohammed ba shi ne mutum na farko da ya fara tattaki zuwa Makka daga Ingila ba. Wani dan Burtaniya Farid Feyadi shi ma ya yi irin wannan tafiya daga Landan a shekarar 2020 don karyata ra’ayoyin da kafafen yada labarai na Yamma suka yi game da Musulunci.

punch news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...
X whatsapp