fidelitybank

Hajjin 2022: Wani mazaunin England ya fara tattaki zuwa Makka

Date:

 

 

Wani haifaffen England, Adam Muhammed, wanda ya fara tattaki a watan Agustan 2021 zuwa aMakka, Saudi Arebiya domin yin aikin Hajji daga Ingila da kafarsa, ya isa yankin Silivri na arewa maso yammacin Turkiyya.

Muhammad ya fara bulaguro ɗin ne, wacce ya yi wa laƙabi da “Tafiya mai aminci”, ya samu taimakon wasu direbobi a kan hanya, inda har ya samu wani kare da ke shawagi kuma tuni su ka zama abokai ya kuma zame masa ɗan rakiya a kasar Sabiya.

Baturen dan asalin kasar Iraqi ya tashi daga Ingila a watan Agustan 2021 zuwa Makka da kafa, balaguron da ya fara da nufin “fito da dukkan munanan abubuwa.”

Muhammad, wanda ke tare da mafaɗacin abokinsa ya ɗaura niyyar isa Saudiyya a lokacin aikin hajji inda ya wuce kasar Siriya sannan ya wuce kasar Jordan kwanaki 35 da wuce Turkiyya.

Yayin da yake zantawa da Kamfanin Dillancin Labarai na Anadolu (AA) game da tafiyar tasa zuwa kasa mai tsarki, Muhammed dan kasar Iraqi da ya kwashe shekaru 25 yana zaune a Ingila ya ce: “Na fara tafiya ne a ranar 1 ga watan Agustan bara. Ina fatan zan yi shi cikin lokaci don aikin hajji na gaba.

“Ina fatan duk tafiyar a kafa ce. Akwai wata murya mai karfi a cikina tana cewa zan iya zuwa Makka ta hanyar tafiya daga gidana. Ba zan iya yin watsi da wannan muryar ba. Yana cikin cikina kamar dutsen mai aman wuta,” in ji shi.

Mohammed ya kara da cewa ya shirya tafiyar tsawon wata biyu kuma wata kungiyar Birtaniya ce ta taimaka masa.

Mohammed ba shi ne mutum na farko da ya fara tattaki zuwa Makka daga Ingila ba. Wani dan Burtaniya Farid Feyadi shi ma ya yi irin wannan tafiya daga Landan a shekarar 2020 don karyata ra’ayoyin da kafafen yada labarai na Yamma suka yi game da Musulunci.

latest news 
in nigeria today 2021 punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp