fidelitybank

Hajjin 2022: Wani mazaunin England ya fara tattaki zuwa Makka

Date:

 

 

Wani haifaffen England, Adam Muhammed, wanda ya fara tattaki a watan Agustan 2021 zuwa aMakka, Saudi Arebiya domin yin aikin Hajji daga Ingila da kafarsa, ya isa yankin Silivri na arewa maso yammacin Turkiyya.

Muhammad ya fara bulaguro ɗin ne, wacce ya yi wa laƙabi da “Tafiya mai aminci”, ya samu taimakon wasu direbobi a kan hanya, inda har ya samu wani kare da ke shawagi kuma tuni su ka zama abokai ya kuma zame masa ɗan rakiya a kasar Sabiya.

Baturen dan asalin kasar Iraqi ya tashi daga Ingila a watan Agustan 2021 zuwa Makka da kafa, balaguron da ya fara da nufin “fito da dukkan munanan abubuwa.”

Muhammad, wanda ke tare da mafaɗacin abokinsa ya ɗaura niyyar isa Saudiyya a lokacin aikin hajji inda ya wuce kasar Siriya sannan ya wuce kasar Jordan kwanaki 35 da wuce Turkiyya.

Yayin da yake zantawa da Kamfanin Dillancin Labarai na Anadolu (AA) game da tafiyar tasa zuwa kasa mai tsarki, Muhammed dan kasar Iraqi da ya kwashe shekaru 25 yana zaune a Ingila ya ce: “Na fara tafiya ne a ranar 1 ga watan Agustan bara. Ina fatan zan yi shi cikin lokaci don aikin hajji na gaba.

“Ina fatan duk tafiyar a kafa ce. Akwai wata murya mai karfi a cikina tana cewa zan iya zuwa Makka ta hanyar tafiya daga gidana. Ba zan iya yin watsi da wannan muryar ba. Yana cikin cikina kamar dutsen mai aman wuta,” in ji shi.

Mohammed ya kara da cewa ya shirya tafiyar tsawon wata biyu kuma wata kungiyar Birtaniya ce ta taimaka masa.

Mohammed ba shi ne mutum na farko da ya fara tattaki zuwa Makka daga Ingila ba. Wani dan Burtaniya Farid Feyadi shi ma ya yi irin wannan tafiya daga Landan a shekarar 2020 don karyata ra’ayoyin da kafafen yada labarai na Yamma suka yi game da Musulunci.

nnnhausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp