fidelitybank

Kotu ta daure magidancin da ya yi wa ‘yar sa ciki

Date:

Kotu a jihar Legas ta daure wani mahaifi mai shekaru 42, zai sha ɗaurin rai-da-rai ba tare da zaɓin biyan tara ba, bayan kotun hukunta laifukan cin zarafi ta same shi da laifin yi wa ‘yarsa mai shekara 15 fyaɗe da kuma yi mata ciki.

Kotun da ke Jihar Legas ta kama Ekpo Lawrence da laifin ne a jiya Alhamis, bayan da mai shari’a, Abiola Soladoye ta ce, kotun ta yi nasarar tabbatar da zargin da gwamnatin Legas ta gabatar kan mista Lawrence.

Kamfanin dillancin labarai na NAN ya rawaito cewa, mai shari’ar ta ce, hujjojin da masu shigar da ƙarar suka bayar sun yi daidai, yayin da shi kuma wanda ake zargi ya yi ta sauya zance.

Ta ƙara da cewa, musanta zargin da mutumin ya yi da gangan ne, domin ya karkatar da hankalin kotu. Ta ce, “Abain kunyar da wanda ake zargin ya aikata ya ƙazanta, kuma ba abin yafewa ba ne a ƙarƙashin sashe na 137 na Dokokin Manyan Laifuka na Jihar Legas na shekarar 2015, sannan abin Allah-wadai ne ta kowace fuska,” in ji Mai Shari’a Soladoye.

kamfanin dillancin labarai na Kasa NAN ta rawaito cewa, masu shigar da ƙara sun ce mutumin ya aikata laifin ne tsakanin watan Disambar shekarar 2018 zuwa watan Yunin 2019.

bbc news 
nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...
X whatsapp