Gwamna jihar Kano, Dr Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana hadarin kwale-kwalen da ya yi sanadiyar mutuwar mutane 20 a matsayin takaici ga jihar.
Dr Ganduje ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da sakataren yada labaran sa, Abba Anwar ya fitar tare da rabawa amnema labarai.
Ya kuma yi addu’ar Allah ya gafartawa mamatan, tare da yin addu’a ga wanda suke kwance a gadon asibiti, ya kuma shawarci matuka kwale-kwale da su kiyaye da yin lodin wuce kima a cikin jirgin ruwa.
Sanarwar ta kara da cewar, Ganduje, ya koka a kan irin wannan lamarin a shekarun baya, ya na mai gargadin cewa, kamata ya yi mutane su sani cewa rayukan ‘yan Adam na da matukar muhimmanci, a dai na ganganci da yin kasada da gangan.