fidelitybank

Hadarin Kwale- Kwale: An tsamo gwarwaki 20 a ruwan Bagwai – Hukumar Kashe Gobara

Date:

Fasinjoji fiye da gawarwakin mutane 20 da aka tsamo a cikin ruwa a wani hadarin kwale-kwale da ya kife a kramar hukumar Bagwai.

Jirgin ruwan ya kife ne a kan hanyarsa ta kauyen Badau zuwa garin Bagwai,ciki harda daliban makarantar Madinatu Islamiyya da ke karamar hukumar Bagwai a jihar Kano.

Daliban da suka rasu, an ce suna kan hanyarsu ta zuwa ne, domin halartar Mauludin da ake gudanarwa duk shekara domin tunawa da haihuwar fiyayyen halitta Annabi Muhammad (S.A.W).

A cewar wata majiya a babban asibitin Bagwai, sama da fasinjoji 40 ne lamarin ya rutsa da su ciki harda daliban makarantar Islamiyya.

Majiyar ta kara da cewa kawo yanzu an gano gawarwaki kimanin 20, kuma an ajiye su a dakin ajiye gawa na asibitin.

Ko a shekarar 2008, fasinjoji 24 ne suka mutu a lokacin da wani kwale-kwale ya kife a kauyen Badau a yayin wani bikin aure.

Mai magana da yawun hukumar kashe gobara ta jihar Kano, SFS Saminu Abdullahi, ya tabbatar da faruwar lamarin, ya kuma kara da cewa hukumar kashe gobara na ci gaba da aikin ceto da misalin karfe 9:15 na dare. Kuma sun gano gawarwakin daliban da abin ya shafa da na sauran fasinjoji 20.

legit ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar Æ´an Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaÉ“e shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka Æ´an Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation HaÉ—in-Kai sun ce sun kashe Æ´an...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aÆ™alla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp