fidelitybank

Hadarin Kwale- Kwale: An tsamo gwarwaki 20 a ruwan Bagwai – Hukumar Kashe Gobara

Date:

Fasinjoji fiye da gawarwakin mutane 20 da aka tsamo a cikin ruwa a wani hadarin kwale-kwale da ya kife a kramar hukumar Bagwai.

Jirgin ruwan ya kife ne a kan hanyarsa ta kauyen Badau zuwa garin Bagwai,ciki harda daliban makarantar Madinatu Islamiyya da ke karamar hukumar Bagwai a jihar Kano.

Daliban da suka rasu, an ce suna kan hanyarsu ta zuwa ne, domin halartar Mauludin da ake gudanarwa duk shekara domin tunawa da haihuwar fiyayyen halitta Annabi Muhammad (S.A.W).

A cewar wata majiya a babban asibitin Bagwai, sama da fasinjoji 40 ne lamarin ya rutsa da su ciki harda daliban makarantar Islamiyya.

Majiyar ta kara da cewa kawo yanzu an gano gawarwaki kimanin 20, kuma an ajiye su a dakin ajiye gawa na asibitin.

Ko a shekarar 2008, fasinjoji 24 ne suka mutu a lokacin da wani kwale-kwale ya kife a kauyen Badau a yayin wani bikin aure.

Mai magana da yawun hukumar kashe gobara ta jihar Kano, SFS Saminu Abdullahi, ya tabbatar da faruwar lamarin, ya kuma kara da cewa hukumar kashe gobara na ci gaba da aikin ceto da misalin karfe 9:15 na dare. Kuma sun gano gawarwakin daliban da abin ya shafa da na sauran fasinjoji 20.

news today in nigeria 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp