fidelitybank

Gwamnonin APC sun nemi Buni da ya ajiye shugabancin jam’iya

Date:

Muryar Gwamnonin APC, PGF, ta yi kira ga Shugaban Jam’iya na Riƙon Ƙwarya, Mai Mala Buni da ya ajiye nukamin sa idan har ba zai kira Babban Taron Jam’iya na Ƙasa a watan Febrairu ba.
Darakta-Janar na PGF, Lukman Salihu ne yai wannan kiran a wata wasiƙa da ya sanyawa hannu a ranar 5 ga watan Janairu.
Daily Nigerian Hausa ta jiyo cewa Salihu ya ce jam’iyar APC na cikin mawuyacin hali, inda ya ƙara da cewa “duk wani yunƙuri na ƙara ɗaga ranar yin Babban Taron Jam’iya na Ƙasa to ya nuna cewa a na wasarere da makomar jam’iyar.”
“Maganganun da su ke fitowa a ciki jam’iyar shine cewa Buni ya na jan kafa wajen yin babban taron domin gwamnonin jihohi na son su ci gaba da juya jam’iyar a Jihohin su.
“Ya kamata manyan jam’iya su kira ganawa ta gaggawa sai a tambayi Buni da sakataren jami’ya, John Akpanudoedehe, a ji menene matsalar kuma wacce barazana su ke fuskanta,” in ji Salihu.
A ƙarshe, Salihu ya ƙalubalanci Buni, wanda shine Gwamnan Jihar Yobe da ya gabatarwa Shugaban Ƙasa kundin rijistar yan jam’iya, inda ya nanata cewa jam’iyar na cikin mawuyacin hali.

vanguard news nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp