fidelitybank

Gwamnonin APC sun nemi Buni da ya ajiye shugabancin jam’iya

Date:

Muryar Gwamnonin APC, PGF, ta yi kira ga Shugaban Jam’iya na Riƙon Ƙwarya, Mai Mala Buni da ya ajiye nukamin sa idan har ba zai kira Babban Taron Jam’iya na Ƙasa a watan Febrairu ba.
Darakta-Janar na PGF, Lukman Salihu ne yai wannan kiran a wata wasiƙa da ya sanyawa hannu a ranar 5 ga watan Janairu.
Daily Nigerian Hausa ta jiyo cewa Salihu ya ce jam’iyar APC na cikin mawuyacin hali, inda ya ƙara da cewa “duk wani yunƙuri na ƙara ɗaga ranar yin Babban Taron Jam’iya na Ƙasa to ya nuna cewa a na wasarere da makomar jam’iyar.”
“Maganganun da su ke fitowa a ciki jam’iyar shine cewa Buni ya na jan kafa wajen yin babban taron domin gwamnonin jihohi na son su ci gaba da juya jam’iyar a Jihohin su.
“Ya kamata manyan jam’iya su kira ganawa ta gaggawa sai a tambayi Buni da sakataren jami’ya, John Akpanudoedehe, a ji menene matsalar kuma wacce barazana su ke fuskanta,” in ji Salihu.
A ƙarshe, Salihu ya ƙalubalanci Buni, wanda shine Gwamnan Jihar Yobe da ya gabatarwa Shugaban Ƙasa kundin rijistar yan jam’iya, inda ya nanata cewa jam’iyar na cikin mawuyacin hali.

nigerian 
news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp