Gwamnatin Jihar Legas ta bada umarnin rufe makarantar Ojodu Grammar School, sakamakon direban Tirela da ya kashe wasu dalibai sama da 15 a ranar Talata, har zuwa watan Janairun 2022.
Hatsarin dai, wanda ya faru da yammacin ranar Talata, ya jawo asarar rayukan dalibai tare da raunata wasu da dama.
Sai dai rundunar ’yan sandan Jihar, ta ce dalibai biyu kacal suka rasa ransu, yayin da kuma dalibai 12 suka ji rauni.
Mai magana da yawun rundunar ’yan sandan Jihar, Adekunle Ajisebutu ne ya tabbatar da hakan ta cikin wata sanarwa da ya fitar.
Ya kuma ce, daliban sun hadu da wasu bata-gari da suka yi kokarin kone ofishin ’yan sanda na yankin Ojodu, sakamakon fusata da suka yi.
Lamarin dai ya sanya ’yan kasuwa da ke kasuwanci a yankin sun rufe shagunansu, domin gudun tashin hankali daga bata-gari.