fidelitybank

Gwamnatin Kano za ta inganta alakarta da Faransa

Date:

Gwamnan Kano Abba Yusuf ya jaddada aniyar gwamnatinsa na inganta dangantakar diflomasiyya da ke tsakanin jihar Kano da kasar Faransa.

Gwamnan ya yi wannan alkawarin ne a wata ganawa da jakadan Faransa a Najeriya a gidan gwamnati ranar Juma’a.

Mataimakin gwamnan jihar, Aminu Gwarzo, wanda ya wakilci gwamnan, ya bayyana irin kokarin da tsohon gwamnan jihar Kano, Rabi’u Musa Kwankwaso ya yi wajen kulla alaka da gwamnatin kasar Faransa.

Gwarzo ya yi tsokaci na musamman da Sanata Kwankwaso ya kafa makarantun sakandare na Faransanci a garin Madobi da wasu biyu a Jamhuriyar Nijar.

A yayin jawabinta, jakadiyar Faransa a Najeriya, Emmanuelle Blatmann ta bayyana cewa ziyarar da tawagar ta kai Kano ita ce gabatar da ayyukan raya kasa daban-daban ga gwamnatin jihar, da nufin samar da ayyukan yi da bunkasa tattalin arzikin jihar.

Blatmann ya kuma yi nuni da cewa, gwamnatin Faransa ta dade tana yin hadin gwiwa a fannin noma a kamfanoni masu zaman kansu, inda ya jaddada inganta ilmin fasahohin aikin gona da koyon sana’o’i ga mata.

Blatmann ya bayyana cewa gwamnatin Faransa ta hannun hukumar raya kasashe ta kasar Faransa ta zuba kudi kusan Euro biliyan uku a wasu ayyuka masu amfani ga ‘yan Najeriya da jihar Kano ke cin gajiyar shekaru 12 da suka gabata.

Wadannan ayyuka sun hada da aikin samar da ruwan sha na birni, aikin motsa jiki, ayyukan makamashi, ayyukan samar da ilimi, aikin sufurin jama’a, da neman gyara/ farfado da cibiyar al’adun Faransa ta Kano, hanyar samun damar shiga karkara da aikin noma (RAAMP) da dai sauransu.

Mataimakin Gwamna Gwarzo, a madadin Gwamna Yusuf, ya tabbatar wa jakadan Faransa cewa gwamnatin jihar Kano za ta yi nazari sosai a kan dukkan ayyukan da aka tsara.

“Daga baya, gwamnatin jihar za ta aika goron gayyata ga gwamnatin Faransa domin tattauna hanyoyin aiwatar da wadannan ayyuka” Abdussalam ya bayyana.

naija news today legits

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp