fidelitybank

Gwamnatin Kano ta na asarar Naira miliyan 378 a kan zaizayar kasa – Dr Gawuna

Date:

Gwamnatin jihar Kano ta bayyana cewa jihar na asarar Naira miliyan 378 a duk shekara, sakamakon zaizayar kasa karkashin aikin noman Watari.

Mataimakin gwamnan jihar, Dr. Nasiru Yusuf Gawuna, ya shaidawa manema labarai jiya a Kano, yayin wani taron manema labarai.

Ya shaida cewa: “Akwai aikin noman ruwa na Watari da aka kammala mai fadin hekta 962 daga cikin kashi 40 cikin 100 ko kuma 384 ba a yi amfani da su a baya ba, saboda lalacewar madatsar ruwa da kayayyakin more rayuwa a can. Amma saboda wannan aikin, APPEALS, ana amfani da shi sosai.

“Akwai kuma gyaran da aka yi na hekta 150 da aka yi a baya, sakamakon zaizayar kasa. An kiyasta asarar hekta 150 a duk shekara ya kai Naira miliyan 378. Sakamakon fadadawar Watari a yanzu haka ta kai hekta 1,000, kuma manoma kusan 4,000 ne za su amfana kai tsaye. Tare da fadada, mun kara amfani da filin noman Watari. Duk da cewa an yi amfani da shi, za mu kaddamar da aikin nan ba da dadewa ba, saboda aiki ne mai matukar muhimmanci,” in ji Gawuna.

Dangane da korafin da manoman jihar suka yi kan rufe madatsar ruwan Tiga da suka ce, ya yi barazana ga ayyukan noman ban ruwa, mataimakin gwamnan ya ce, ana sa ran kammala aikin dam a tsakiyar wannan shekara.

Dr. Nasiru Yusuf Gawuna, wanda ke rike da mukamin kwamishinan noma da albarkatun kasa na jihar, ya ce, an rufe dam din ne domin a samu damar yin gyare-gyare a madatsar, domin samun cikakken amfani da bunkasa ayyukan noman ban ruwa a yankunan.

latest news in nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp