fidelitybank

Gwamnatin Kano ta kulla yarjejeniya da kasar Saudiyya na horar da malamai 5,000

Date:

Gwamnatin jihar Kano karkashin Dr. Abdullahi Ganduje ta amince da wata yarjejeniya tsakanin Kano da Madina Academy da ke kasar Saudiyya, domin horar da malamai 5,000 a Madina.

Gwamnatin jihar za ta dauki nauyin bayar da tikitin dawowar jirgi, biza, alawus na horo ga rukunin farko na malamai 50 da za su halarci babban horo a Madina kafin watan Ramadan.

Gwamnatin ta kuma amince da fitar da Naira miliyan 94.9 domin saukaka matsugunin shagunan haya da gareji a kasar Saudiyya na shekarar 2020 da 2021.

A halin da a ke ciki, gwamnatin Ganduje ta kuma amince da Naira miliyan 500 a matsayin asusun tallafi na shekara shida na bankin duniya, mai suna ‘Agro Climatic Resilience in Semi-Arid Landscapes (ACReSAL)’.

Kwamishinan yada labarai, Muhammad Garba ne ya sanar da hakan a yayin ganawa da manema labarai kan sakamakon taron majalisar zartarwar jihar na jihar.

Ya yi bayanin cewa aikin na da nufin kara daukar sabbin hanyoyin magance yanayi da inganta rayuwa tare da magance kwaranyowar hamada a Arewacin Najeriya.

Aikin zai karfafa nasarorin da a ka samu a karkashin shirin kula da zaizayar kasa da ruwan sha ta Najeriya (NEWMAP) a Kano.

Kwamishinan ya ci gaba da bayyana cewa majalisar ta amince da kwangilar kammala aikin gyaran hanya mai tsawon kilomita biyar a karamar hukumar Tofa.

Wani amincewa kuma shine domin sakin kudade don horar da ma’aikatan kiwon lafiya da kuma mayar da tallafin asusun ilimi mai kunshe da stamfi.

Ya kara da cewa majalisar ta amince da sabunta sadarwar intanet da kuma kula da kayan aikin fasahar ICT mai kunshe da bayanan hukumar lura da asibitoci (HMIS) wanda za kuma a sanya manhajar software a asibitin koyarwa na Abdullahi Wase.

Sauran sun kasance masu ba da shawara ne domin kula da shirin samar da hanyoyin sadarwa na Fiber Optics na jihar Kano da kuma siyan motocin kashe gobara.

vanguard 
nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuÉ—in gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuÉ—in gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuÉ—a

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiÉ—a wa Isra'ila wasu...
X whatsapp