fidelitybank

Gwamnatin Kano ta kulla yarjejeniya da kasar Saudiyya na horar da malamai 5,000

Date:

Gwamnatin jihar Kano karkashin Dr. Abdullahi Ganduje ta amince da wata yarjejeniya tsakanin Kano da Madina Academy da ke kasar Saudiyya, domin horar da malamai 5,000 a Madina.

Gwamnatin jihar za ta dauki nauyin bayar da tikitin dawowar jirgi, biza, alawus na horo ga rukunin farko na malamai 50 da za su halarci babban horo a Madina kafin watan Ramadan.

Gwamnatin ta kuma amince da fitar da Naira miliyan 94.9 domin saukaka matsugunin shagunan haya da gareji a kasar Saudiyya na shekarar 2020 da 2021.

A halin da a ke ciki, gwamnatin Ganduje ta kuma amince da Naira miliyan 500 a matsayin asusun tallafi na shekara shida na bankin duniya, mai suna ‘Agro Climatic Resilience in Semi-Arid Landscapes (ACReSAL)’.

Kwamishinan yada labarai, Muhammad Garba ne ya sanar da hakan a yayin ganawa da manema labarai kan sakamakon taron majalisar zartarwar jihar na jihar.

Ya yi bayanin cewa aikin na da nufin kara daukar sabbin hanyoyin magance yanayi da inganta rayuwa tare da magance kwaranyowar hamada a Arewacin Najeriya.

Aikin zai karfafa nasarorin da a ka samu a karkashin shirin kula da zaizayar kasa da ruwan sha ta Najeriya (NEWMAP) a Kano.

Kwamishinan ya ci gaba da bayyana cewa majalisar ta amince da kwangilar kammala aikin gyaran hanya mai tsawon kilomita biyar a karamar hukumar Tofa.

Wani amincewa kuma shine domin sakin kudade don horar da ma’aikatan kiwon lafiya da kuma mayar da tallafin asusun ilimi mai kunshe da stamfi.

Ya kara da cewa majalisar ta amince da sabunta sadarwar intanet da kuma kula da kayan aikin fasahar ICT mai kunshe da bayanan hukumar lura da asibitoci (HMIS) wanda za kuma a sanya manhajar software a asibitin koyarwa na Abdullahi Wase.

Sauran sun kasance masu ba da shawara ne domin kula da shirin samar da hanyoyin sadarwa na Fiber Optics na jihar Kano da kuma siyan motocin kashe gobara.

vgn news today 2021

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaÉ—an wajen tsaron Æ™asa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haÉ—in...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar Æ´an Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaÉ“e shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka Æ´an Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation HaÉ—in-Kai sun ce sun kashe Æ´an...
X whatsapp