fidelitybank

Gwamnatin Kano ta kara fadada shirin matasa 

Date:

Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano ya sake, tabbatar da kudurin gwamnatinsa na karfafa matasa ta hanyar samar da ayyukan yi masu ɗorewa, fadada damar koyon sana’o’i, da kuma ƙarfafa yaki da amfani da miyagun kwayoyi.

Gwamnan ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Laraba, domin tunawa da Ranar Matasa ta Duniya a wannan shekara.

“Matasa su ne ginshiƙin canjin tattalin arziki da zamantakewa a Kano,” in ji Gwamna Yusuf. “Mun sake buɗe cibiyoyin koyon sana’o’i a fannoni daban-daban, wanda hakan ya ba dubban matasanmu damar dogaro da kansu.”

Haka kuma, an samar da damar aiki kai tsaye a muhimman sassa kamar kiwon lafiya, ilimi, aikin gona, da ayyukan gwamnati.

Gwamnan ya kuma bayyana shirin sake buɗe Cibiyar Gyara Hali na Kiru domin gyara da dawo da matasa masu laifi musamman waɗanda ke fama da amfani da miyagun kwayoyi.

A bangaren Fasahar Sadarwa da Kwamfuta (ICT), Yusuf ya jaddada nasarorin da aka samu ta kafuwar Hukumar KASITDA da kuma nasarar shirya Taron Kasa da Kasa kan Fasaha da Kwamfuta.

Ya bayyana waɗannan a matsayin muhimman matakai don sanya Kano cibiyar ƙirƙira da kwarewar dijital.

“A wannan Ranar Matasa ta Duniya, muna murnar juriya, ƙirƙira, da ƙarfin matasanmu,” in ji gwamnan. “Gwamnatina za ta ci gaba da zuba jari a makomar su ta hanyar samar da ayyukan yi, ilimi, fasaha, da yaki da miyagun kwayoyi.”

Gwamna Yusuf ya yi kira ga shugabannin al’umma, malamai, iyaye, sassan masu zaman kansu, da sauran masu ruwa da tsaki su haɗa kai wajen samar da yanayi mai aminci, haɗin kai, da wadata domin matasan Kano su cika burinsu cikin cikakken iko.

legitnews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp