fidelitybank

Gwamnatin Kano ta gargadi Matasa da ‘yan Gwangwan kan sayen kayan gwamnati

Date:

Gwamnatin Jihar Kano ta gargadi matasa da ’yan kasuwa da ke siyarwa ko sayen kayan gwamnati da aka sace, musamman ƙarafunan fitilun titi, wayoyin lantarki da sauran kayayyakin da aka tanadar a tituna.

Wannan na cikin sanarwar da Khamis Bashir Bako Ayagi, mai ɗauko wa gwamna rahoto a Ma’aikatar Ayyuka ta Jihar Kano, ya fitar a ranar Litinin, 25 ga Agusta, 2025 a Kano.

Sanarwar ta ce Gwamna Abba Kabir Yusuf ya umarci ma’aikatar ayyuka ta tattaunawa da shugabannin masu sana’ar saye da sarrafa ƙarafa a jihar.
Haka kuma an kafa kwamitin da ya ƙunshi jami’an tsaro da sauran hukumomi domin dakile wannan matsala.

Gwamnatin ta jaddada cewa duk wanda aka kama da kayan gwamnati da aka sace, ko mai siyan su daga hannun barayi, za a ɗauki matakin doka a kansa.
Sanarwar ta kuma yi kira ga iyaye, shugabannin unguwanni da masu fada a ji su ja kunnen ’ya’yansu, tare da gargadin ’yan kasuwa da su guji siyan kayayyakin da aka sace daga wuraren gwamnati.

latest news in lokoja, kogi state

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp