Gwamnatin Najeriya ta ce za ta tura wa majalisar dokoki, bukatar yin gyara ga dokar harkokin man fetur ta kasar, domin tsawaita wa’adin cire tallafin man da wata 18.
Karamin Ministan Harkokin Man Fetur, Timipreye Silva wanda ya sanar da hakan a wajen wani taron manema labarai a fadar shugaban kasa.
Ya ce“A ranar 16 ga watan gobe na Febrairu, ya kamata a janye tallafin, bisa dokar wadda aka saka wa hannu a ranar 16 ga watan Augustan shekarar da ta wuce.
Sai dai ya ce, “Saboda rashin tattalin wasu abubuwa da dokar ta tanada a samar kafin cire tallafin hakan bai zai yiwu kafin nan da mako uku ba”. In ji Timpireye.