fidelitybank

Gwamnati za ta kashe Naira biliyan 250 don yaƙar Talauci

Date:

Mataimakin shugaban ƙasa, Yemi Osinbajo ne ya bayyana hakan a yayin wani bayani da ya yi kan rahoton ci gaban da aka samu a shirin rage talaucin na ƙasa da ake kira NPRGS a gaban kwamitin da ya jagoranta a ranar Laraba.

Ayyuakan da aka tsara aiwatarwa a bana ƙarƙashin NPRGS sun haɗa da: “Gina gidaje dubu ɗari ga masu ƙaramin ƙarfi, wanda zai samar da ayyukan yi miliyan ɗaya na kai-tsaye ko a fakaice.

“Faɗaɗa samun makamashi ta hanyar samar da fitilun gefen titi 1,200 a yankunan karkara da kuma wasu ƙananan tashoshin wuta da za a riƙa amfani da su a gonaki ƙarƙashin shirin Solar Naija.

“Samar da ayyuka miliyan huɗu da ɗari biyar na kai-tsaye ko kuma a fakaice ta hanyar shirin gina hanyoyi a yankin karkara waɗanda za su haɗa kasuwannin ƙauye 750 a faɗin Najeriya.

“Samar da taimakon naira biliyan tara ga masu gonakin da ba su da karfi a lokacin daminar bana karkashin shirin samar da akin yi a bangaren noma.

“Fadada rajistar mutanen da ke samun tallafin rayuwa da karin sunayen magidanta miliyan uku.”

A lokacin gabatar da bayanin, Ministan kasafin kudi da tsare tsare, Clem Agba, ya ce mutum miliyan biyu ne suka amfana da shirin NPRGS kai-tsaye a 2022.

Rahotansa ya bayyana cewa manoma miliyan daya da dubu 600 ne suka mafana da shirin karkashin shirin habbaka noma.

Cikin wata sanarwa da mai magana da yawun mataimakin shugaban Najeriyan ya fitar a jiya, ya ce matasa 13,000 sun samu horo kan kere-kere da kuma sana’o’in hannu a jihohi 6 da suka hada da Legas da Ogun da Enugu da Gombe da Kaduna da Nasarawa, yayin da ake shirin samar da irin wannan tsari ga matasa 2,000 a jihar Edo.

Ya ce sama da ‘yan Najeriya 8,000 aka ɗauka aikin shimfiɗa tituna a yankin karkara ƙarƙashin shirin samar da hanyoyi a karkara, inda aka gina hanyoyi 40 cikin kauyuka 120 a faɗin Najeriya.

“A duka Najeriya mutum 1,818,782 ne suke cin gajiyar shirin NPRGS, kuma an ɗauki mutum 9,527 aiki ƙarƙashin aikin ya zuwa yanzu.”

newstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp