Ministan Sufurin Jiragen Sama da Cigaban Jiragen Sama Festus Keyamo, ya ce Gwamnatin Najeriya na kashe Naira Biliyan 1 wajen biyan tallafin kudin alawus na Duty Tour Allowance (DTA) da tikitin jirgin sama ga Hukumar Kula da Jiragen Sama ta Tarayyar Najeriya, FAAN, jamiāan da ke kai da kawowa daga Abuja zuwa Legas, duk shekara.
Keyamo ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis a wata sanarwa da ya fitar da ke fayyace kalamansa na āDTA maāaikatan FAAN N500 a gidan Talabijin na Channels.
A cewarsa, a shekarar 2023 maāaikatan FAAN sun kashe N493,678,620.37 akan DTA da kuma N451,058,950.09 na tikitin jirgi.
āLokacin da na yi hira da gidan talabijin na Channels a jiya, ba a yi mini bayani ba game da kudaden da FAAN ta kashe a shekarar da ta gabata a kan DTA (Duty Tour Allowance) ga manyan jamiāan da ke kai da komowa daga Legas zuwa Abuja kusan kullum.
āKudin ya kai N493,678,620.37. Baya ga tikitin jirgin da na ambata ya kai N451,058,950.09.
āDon haka, a dunkule, saboda dagewar da aka yi na nada Abuja a matsayin hedikwatar FAAN (lokacin da babu ofisoshi a Abuja da zai dauki dukkan manyan jamiāan FAAN), FAAN ta kashe kusan Naira biliyan daya a shekara guda,ā inji shi.
DAILY POST ta rahoto cewa Ministan ya dage kan ci gaba da matakin da Gwamnatin Tarayya ta dauka na mayar da hedikwatar FAAN zuwa Legas duk da adawar da wasu bangarorin suka yi.
Ku tuna cewa a ranar 19 ga watan Janairu, 2023, Keyamo ya sanar da sauya shelkwatar FAAN daga Abuja zuwa Legas.