Cibiyar kirkire-kirkire da ci gaban aikin jarida, CJID, ta shawarci gwamnatin Najeriya da ta mutunta tare da kare ‘yancin ‘yan jarida, ta yadda ‘yan jarida za su yi aiki cikin walwala ba tare da cin zarafi ba kafin, lokacin da kuma bayan zaben 2023.
Cibiyar ta kara da cewa ya kamata gwamnati ta tabbatar da cewa ba a cin zarafin ‘yan jarida ko kuma tsoratar da ‘yan jarida a yayin da suke yada labaran zabe kamar yadda aka yi a zabukan da suka gabata.
Shugaban harkokin siyasa a babbar hukumar Kanada a Najeriya, Andy Web ne ya yi wannan kiran yayin jawabinsa a wani taron manema labarai mai taken “Zaben 2023: Tsaro, Kafafen Yada Labarai da Safety,” a karshen mako.
Karanta Wannan: Ƙungiyar Kiristoci ta jinjina wa Buhari a kan zaɓen 2023
Babban kwamishinan yayin da yake lura da cewa wasu jami’an gwamnatin Najeriya na amfani da son zuciya wajen magance rikice-rikicen kafafen yada labarai da hukumomin kasar, yana mai ba da tabbacin gwamnatin Canada na goyon bayan ‘yancin yada labarai a Najeriya a kowane lokaci.
Ya ce: “Muna kira ga gwamnati da ta mutunta ‘yancin yada labarai domin ‘yan jarida su yi aiki cikin walwala ba tare da an ci zarafinsu ba.
“Taron shine don tunawa da ranar duniya don kawo karshen rashin hukunta masu aikata laifukan da ake yi wa ‘yan jarida kuma martani ne ga ci gaba da barazana ga tsaron lafiyar ‘yan jarida, da kuma fargabar abin da ka iya tasowa bayan zabukan 2023 a kasar.”
Babban mai jawabi, Farfesa Umaru Pate, mataimakin shugaban jami’ar tarayya Kashere, ya bayyana cewa zabuka a Najeriya na da matukar hadari da tashin hankali, inda ya yi nadamar cewa ‘yan jarida ne suka fi fuskantar matsalar.
Ya kara da cewa, a zaben 2019 an ci zarafin wasu ‘yan jarida tare da tsare wasu gidajen yanar gizo guda 20, tare da tsoratarwa, ba tare da wani yunkurin gurfanar da wadanda suka aikata laifin a gaban kuliya ba.
“Wannan zai sa ƙungiyoyin watsa labarai su kasance masu yin katsalandan da kansu wanda ke raunana aikin jarida na bincike,” in ji shi.