fidelitybank

Gwamnati da ASUU su warware matasalar yajin aiki – Sanusi

Date:

Tsohon gwamnan babban bankin Najeriya (CBN), Lamido Sanusi, ya bukaci gwamnatin tarayya da kungiyar malaman jami’o’i (ASUU) da su warware rikicin da ya dabaibaye su a kan yajin aiki.

Sanusi ya yi wannan kiran ne a wata hira da ya yi da Kamfanin Dillancin Labarai na kasa a birnin New York na kasar Amurka, a ci gaba da taron koli na sauya fasalin ilimi na kwanaki uku.

Sanusi ya ce za a iya magance yajin aikin ASUU ta hanyar tattaunawa, yana mai cewa akwai bukatar kungiyar ta san cewa tsawon lokacin da ta aka yi ba a zuwa makaranta, daliban ne za su sha wahala.

“Ya kamata gwamnati ta gane cewa malamai mutane ne; muna cikin kasar da ake fama da hauhawar farashi kuma albashi ba ya kai malamai ko’ina kuma koyarwa sana’a ce da ya kamata a ba ta daraja daga mafi karanci zuwa babba.

“Ma’aikatanmu na ilimi ma’aikatan kiwon lafiya ne ma, abin da ba mu sani ba shi ne mun yi asarar malamai da yawa, yawancin mutanen da ke fita kasashen waje don yin PhD ba sa dawowa.

“Likitoci da yawa da ke aiki a Najeriya sun fita kasashen waje,” in ji shi.

Tsohon shugaban babban bankin na CBN, wanda shine Sarkin Kano na 14, ya ce zubar da kwakwalwa ya yi illa ga tattalin arziki.

“Rikici ne saboda muna bukatar likitoci a Najeriya, muna bukatar malamai a Najeriya saboda mun saka jari sosai wajen horar da su.

“Dukan bangarorin biyu (ASUU da Gwamnatin Tarayya) suna da ruwa da tsaki wajen zama a yi tattaunawa, yin sulhu, na yi imanin za a iya warware shi cikin gaskiya,” inji shi.

Sanusi ya kuma bukaci gwamnati da ta saka hannun jari a fannin ilimi domin karfafa gwiwar malamai su kasance masu iya kokarinsu, ya kara da cewa a lokutan baya malamai sun kasance suna mutunta daraja a cikin al’umma a baya, ya kara da cewa “amma yanzu mutane sun raina darajar ilimi.

mmm.nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...
X whatsapp