fidelitybank

Gwamnan Yobe ya janye dokar hawa Babur a jihar bayan shekaru 10

Date:

Gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni ya dage dokar hana amfani da babura a yankunan Arewaci da Kudancin jihar.

Hakan dai ya biyo bayan komawar al’amura a galibin yankunan tare da komawar hukumomin farar hula.

Gwamnan ya bayyana haka ne a lokacin da ya kai ziyara fadar Sarkin Nguru, domin jajanta wa jama’a kan aukuwar gobara da ta lalata kadarori na miliyoyin Naira a kasuwar Nguru.

Buni ya ce”A yanzu mazauna garin sun samu damar hawan Babura, domin gudanar da harkokinsu na yau da kullum.

“Da wannan ne mu ke gudanar da wani bangare na yakin neman zabe, domin dawo da zaman lafiya a jihar da kuma ba da damar amfani da Babura, domin bukatun jama’a,” inji shi.

Kananan hukumomi 10 da aka amince su yi amfani da baburan sun hada da Fika, Nangere, Fune, Potiskum, Jakusko, Bade, Nguru, Karasuwa, Yusufari da Machina.

Sai dai matakin ya ta’allaka ne da wasu sharudda takwas da masu tuka mota suka cika, daya daga cikinsu shi ne cewa dole ne su rika gudanar da aiki daga karfe shida na safe zuwa karfe 6 na yamma a kowace rana kuma kada a yi amfani da su wajen tallan kabu-kabu (Achaba). Mahayi daya ne kawai za a yarda ba tare da wani mutum a kan babur ba.

Ya ce”Dole ne a samar da ingantaccen rajista, lasisi da takaddun duk babura da masu keke a cikin kananan hukumomin da hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa ta jihar Yobe (YROTA) ke aiwatarwa”. A cewar Buni.

Idan dai za a iya tunawa gwamnatin jihar Yobe ta haramta amfani da babura a daidai lokacin da rikicin Boko Haram ya barke a cikin shekaru 12 da suka gabata.

vanguard newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Duk wani tuggun ku Atiku da El-Rufa’i ba za ku iya kayar da Tinubu ba – Bwala

Fadar shugaban kasa ta yi watsi da kokarin da...

Mutuwar Dantata ta girgiza kasa baki daya – Tinubu

Shugaban kasa Ahmad Bola Tinubu ya bayyana Alhaji Aminu...

Wike ya caccaki Rotimi a kan jam’iyyar ADC

Ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, ya caccaki tsohon...

Tsige ni daga mukamin Wazirin Gaya ba a kan doka ba ne – Usman Alhaji

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Kano, Alhaji Usman Alhaji, ya...

Gini mai bene uku ya danne Mutane a jihar Legas

Wani gini mai bene uku ya rufta a unguwar...

Kotu ta daure Matashi dan Tiktok da ya ke sanya rigar mama

Wata kotu a jihar Kano, ta yanke wa wani...

Peter Obi ka gaggauta ficewa daga jam’iyyar mu nan da awa 48 – Labour Party

Bangaren jam’iyyar Labour da Julius Abure ke jagoranta, ya...

Lakurawa sun kashe Mutane 15 a Sokoto

Wasu da ake zargin mambobin ƙungiyar Lakurawa ne sun...

Dan wasan Liverpool Diago Jota da Kaninsa sun mu a hadarin mota

Ɗan wasan ƙwallon ƙafar Liverpool kuma ɗan ƙasar Portugal,...

Mun shirya tunkarar APC a 2027 – ADC

A ranar Laraba ne manyan ƴan adawar siyasa suka...

Mun dagulawa Iran lisafi na tsawon shekaru biyu a nukiliyar ta – Amurka

Ma'aikatar tsaron Amurka ta ce bayannan leken asirinta ya...

INEC za ta fitar da sabbin ƙa’idojin duba sakamakon zaɓe

A shirye-shiryen da take yi gabanin babban zaɓen Najeriya...
X whatsapp