Gwamnan Jihar Kaduna Malam Uba Sani ya mayar wa Jonathan Paragua Zamuna rawaninsa na Sarkin Piriga.
Gwamnan ya ce ya mayar wa sarkin rawaninsa ne bayan kotun ma’aikata ta jihar ta yanke hukuncin soke cire masa rawanin.
A zamanin tsohon gwamnan jihar, Nasiru El-Rufai ne aka tuɓe rawanin sarkin, amma daga bisani sarkin ya kai ƙara kotu, inda a ranar 14 ga Yunin 2024, kotu ta soke cire sarkin, kamar yadda Channels ta ruwaito.
Uba Sani ya taya sarkin murnar komawa kujerarsa, sannan ya yi kira a gare shi da ya yi adalci ga kowa ba tare da nuna bambancin addini da ƙabila.
“Gwamnatinmu tana bin doka da oda. Wannan ne ya sa ba mu ɓata lokaci ba wajen ɗabbaƙa hukuncin kotun ma’aikata na mayar wa Sarkin Piriga rawaninsa,” in ji shi.
A nasa ɓangare, Sarkin Piriga, ya yi godiya ga gwamnan bisa mayar masa da rawani, inda ya ƙara da cewa akwai ƙabilu 12, kuma suna zama lafiya tare da juna.