fidelitybank

Gwamnan Kaduna ya dawo da rawanin Sarkin da El-Rufa’i ya tsige

Date:

Gwamnan Jihar Kaduna Malam Uba Sani ya mayar wa Jonathan Paragua Zamuna rawaninsa na Sarkin Piriga.

 

Gwamnan ya ce ya mayar wa sarkin rawaninsa ne bayan kotun ma’aikata ta jihar ta yanke hukuncin soke cire masa rawanin.

 

A zamanin tsohon gwamnan jihar, Nasiru El-Rufai ne aka tuɓe rawanin sarkin, amma daga bisani sarkin ya kai ƙara kotu, inda a ranar 14 ga Yunin 2024, kotu ta soke cire sarkin, kamar yadda Channels ta ruwaito.

 

Uba Sani ya taya sarkin murnar komawa kujerarsa, sannan ya yi kira a gare shi da ya yi adalci ga kowa ba tare da nuna bambancin addini da ƙabila.

 

“Gwamnatinmu tana bin doka da oda. Wannan ne ya sa ba mu ɓata lokaci ba wajen ɗabbaƙa hukuncin kotun ma’aikata na mayar wa Sarkin Piriga rawaninsa,” in ji shi.

 

A nasa ɓangare, Sarkin Piriga, ya yi godiya ga gwamnan bisa mayar masa da rawani, inda ya ƙara da cewa akwai ƙabilu 12, kuma suna zama lafiya tare da juna.

legit.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp