Likitocin Abuja waɗanda suke yajin aiki sun ƙalubalanci Ministan Abuja Nyesome Wike da Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio su riƙa amfani da asibitocin gwamnati da ke babban birnin tarayya, Abuja domin sanin halin da marasa lafiya suke shiga.
“Idan mun shirya gyara ɓangaren kiwon lafiya a ƙasar nan, ina tunanin ya kamata a tilasta wa jami’an gwamnati amfani da asibitocin gwamnati,” kamar yadda shugaban ƙungiyar likitocin Abuja, George Ebong ya bayyana a tattaunawarsa da tashar Channels a ranar Laraba.
“Zan so in fara ganin ministan yana zuwa asibitin Wuse, zan so ganin shugaban majalisar dattawa yana zuwa asibitin Maitama, sannan mu ga shugaban majalisar wakilai yana zuwa asibitin Nyanya. Idan aka fara haka ne za a iya gyara ɓangaren kiwon lafiya, amma matuƙar ba sa amfani da su, maganar gaskiya ba za a iya gyara su.”
Tun da farko, likitocin na Abuja sun faɗa yajin aiki ne a ranar Laraba saboda wasu haƙƙoƙinsu bayan wa’adin mako uku da suka bayar ya ƙare.