fidelitybank

Gwamnan Bauchi ka manta da batun takarar shugaban kasa – CAN

Date:

Mabiya addinin Kirista a jihar Bauchi sun shaida wa Gwamna jihar, Bala Mohammed cewa ya yi watsi da duk wani shiri na tsayawa takarar shugaban kasa a 2023.

Shugaban kungiyar kuma shugaban kungiyar kiristoci ta Najeriya (CAN), Reverend Abraham Damina Dimeus ne ya bayyana hakan a ranar Asabar a lokacin da ya ke jawabi a gidan gwamnati da ke Bauchi.

Kiristocin sun bi sahun gwamnan domin bikin Kirsimeti na bana.

Malamin ya ce mutanen yankin na jin dadin zaman gwamnan, domin haka ya kamata ya sake tsayawa takara a karo na biyu maimakon ya zubawa shugaban kasa ido.

“Duk da cewa a shirye mu ke mu tafi tare da ku a duk inda ku ka je, amma a halin yanzu muna bukatar ku ci gaba da zama a nan Jihar Bauchi, domin kammala aikin da kuka fara.

“Al’ummar Kirista na jin daÉ—in mulkin ku tun lokacin da ku ka hau mulki. Ba ku nuna wariya ga al’ummar Kirista ba. Kun tafiyar da mu a cikin harkokin mulki,” inji Rev Dimeus.

Gwamna Mohammed ya nuna godiya ga Allah da ya baiwa kowa damar sake yin wani bikin Kirsimeti, ya na mai bayyana hakan a matsayin alheri da rahamar Ubangiji.

Gwamnan ya ce, ba shi da wani zabi illa ya yi wa kowa a jihar daidai wa daida ba tare da la’akari da addininsa ba, domin shi dan gida ne da ke da Musulmi da Kirista.

vanguard newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar Æ´an Æ™asarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan ÆŠaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp