Mabiya addinin Kirista a jihar Bauchi sun shaida wa Gwamna jihar, Bala Mohammed cewa ya yi watsi da duk wani shiri na tsayawa takarar shugaban kasa a 2023.
Shugaban kungiyar kuma shugaban kungiyar kiristoci ta Najeriya (CAN), Reverend Abraham Damina Dimeus ne ya bayyana hakan a ranar Asabar a lokacin da ya ke jawabi a gidan gwamnati da ke Bauchi.
Kiristocin sun bi sahun gwamnan domin bikin Kirsimeti na bana.
Malamin ya ce mutanen yankin na jin dadin zaman gwamnan, domin haka ya kamata ya sake tsayawa takara a karo na biyu maimakon ya zubawa shugaban kasa ido.
“Duk da cewa a shirye mu ke mu tafi tare da ku a duk inda ku ka je, amma a halin yanzu muna bukatar ku ci gaba da zama a nan Jihar Bauchi, domin kammala aikin da kuka fara.
“Al’ummar Kirista na jin daÉ—in mulkin ku tun lokacin da ku ka hau mulki. Ba ku nuna wariya ga al’ummar Kirista ba. Kun tafiyar da mu a cikin harkokin mulki,” inji Rev Dimeus.
Gwamna Mohammed ya nuna godiya ga Allah da ya baiwa kowa damar sake yin wani bikin Kirsimeti, ya na mai bayyana hakan a matsayin alheri da rahamar Ubangiji.
Gwamnan ya ce, ba shi da wani zabi illa ya yi wa kowa a jihar daidai wa daida ba tare da la’akari da addininsa ba, domin shi dan gida ne da ke da Musulmi da Kirista.