fidelitybank

Gwamna ya hana mataimakinsa shiga ofishinsa

Date:

An hana mataimakin gwamnan jihar Edo, Philip Shaibu, shiga ofishinsa da ke gidan gwamnati a Benin babban birnin jihar.

Gidan Talabijin na Channels ya ruwaito cewa, Shaibu ya isa gidan gwamnatin ne da safiyar yau Litinin, inda ya iske kofar shiga ofishin nasa a kulle.

Ya ce bai samu wata takarda daga ofishin gwamnan ba, da ke umurtar sa da sauya wurin aiki, wanda kuma ita ce ya kamata ta zama hanyar ba shi umarnin barin ofishinsa da ke gidan gwamnati.

“Har yanzu ban samu wata sanarwa ba a hukumance da aka umarce ni na canza ofis.

“Ma’aikatan ofis dina ne kawai suka samu saƙon, ba ni ba.”

“A yanzu haka da nake magana da ku, ina tsaye a bakin kofa,” in ji shi yayin da yake tattaunawa da wani wanda ba a san ko wane ne ba.

A makon da ya gabata, an aika da wata wasiƙa daga ofishin shugaban ma’aikata na gidan gwamnatin jihar, wadda ke ɗauke da saƙon umurni ga mataimakin gwamna, Philip Shu’aibu kan cewa an mayar da ofishinsa zuwa gini mai lamba 7, Dennis Osadebey Avenue, GRA, Benin City.

breaking news in nigeria today 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp