fidelitybank

Gwamna mai jiran gado Soludo ya nada kwamitin rantsar da shi

Date:

Zababben gwamnan jihar Anambra, Farfesa Chukwuma Soludo, ya fitar da jerin sunayen mambobin kwamitin mika mulki mai wakilai 80 da za su taimaka wajen rantsar da shi a ranar 17 ga Maris, 2022.

A cikin wata sanarwa da ya fitar, jiya, ta hannun mai taimaka wa Soludo kan harkokin yada labarai, Joe Anatume, jerin sun kunshi mambobi 80, tare da fitattun ‘yan Najeriya, wadanda za su taka rawa daban-daban.

Ya ce, kwamitin zai tuntubi tawagar da gwamnatin jihar Anambra ta kafa, domin tabbatar da karbar mulki daga hannun gwamnatin Willie Obiano zuwa gwamnatin Soludo daga ranar 17 ga Maris, 2022.

Sanarwar ta tabbatar da cewa, tsohuwar ministar ilimi, Dr. Oby Ezekwesili, ita ce shugabar kwamitin, yayin da Farfesa Benedict Oramah, Farfesa Pat Utomi da Osita Chidoka za su taka muhimmiyar rawa wajen shirin mika mulki.

Sauran mambobin sun hada da: Uche Okafor, Farfesa Chidi Odinkalu, Steve Nworga, Ben Nwankwo, Charles Odedo, Tony Ifeanya, Ferdinand Agu, Farfesa Osita Ogbu, Chikwe Udensi, Greg Ibe da Alex Otti, da dai sauransu.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, za a sanar da sharuddan kwamitin, da kuma yadda za a gudanar da shi a yayin kaddamar da taron farko da kuma zaman taron farko da aka shirya gudanarwa tsakanin 19 da 22 ga watan Janairu, 2022 a otal din Golden Tulip (Agulu Lake) da ke cikin Otal din Golden Tulip (Agulu Lake) jihar

Har ila yau, ya ce, a na sa ran mambobin za su isa ranar Laraba 19 ga watan Janairu, yayin da za a fara taron kaddamar da taron farko a ranar 20 ga watan Janairu.

nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta...

An kashe mutane 10 a wani sabon rikici da ya ɓarke a Filato

Aƙalla mutabe 10 ne aka kashe tare da sace...

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta...

Hauhawar farashi ya ragu da kaso 23.71 a Najeriya – NBS

An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga...

Fiye da mutane 100 Makiyaya aka kashe a Jos

An ruwaito cewa an kashe wani makiyayi guda da...

Tinubu ka kori shugaban JAMB – Sowore

Dan siyasa mai fafutuka, Omoyele Sowore, ya yi kira...

Majalisa ta yi watsi da ƙudirin karɓa-karɓa

Majalisar wakilai ta yi watsi da wani ƙudirin doka...

Labarin mu na kaiwa Ƴan Bindiga abinci Æ™arya ne – Ƴansanda

Rundunar Æ´ansandan Najeriya ta musanta rahotannin da ake yaÉ—awa...

Ba za mu yarda mu mutu a cikin PDP ba shi yasa muka koma APC – Sanatoci

Sanatocin Najeriya uku da suka fito daga jihar Kebbi,...

Sojoji sun tarwatsa wajen da ake hakar man fetur ba bisa ka’ida ba a Rivers

Rundunar Sojin Ruwa ta Najeriya, NNS, Pathfinder, ta tarwatsa...

Dan Tinubu Seyi da sauran ‘yan Siyasa sun fara neman kujerar gwamnan Legas

Siyasar Legas na kara ruruwa na neman maye gurbin...

Mayakan IS sun yi wa Sojojin Najeriya barna a kwana biyu

Mayaƙan IS sun ƙara kai wa sojojin Najeriya hari,...
X whatsapp