Zababben gwamnan jihar Anambra, Farfesa Chukwuma Soludo, ya fitar da jerin sunayen mambobin kwamitin mika mulki mai wakilai 80 da za su taimaka wajen rantsar da shi a ranar 17 ga Maris, 2022.
A cikin wata sanarwa da ya fitar, jiya, ta hannun mai taimaka wa Soludo kan harkokin yada labarai, Joe Anatume, jerin sun kunshi mambobi 80, tare da fitattun ‘yan Najeriya, wadanda za su taka rawa daban-daban.
Ya ce, kwamitin zai tuntubi tawagar da gwamnatin jihar Anambra ta kafa, domin tabbatar da karbar mulki daga hannun gwamnatin Willie Obiano zuwa gwamnatin Soludo daga ranar 17 ga Maris, 2022.
Sanarwar ta tabbatar da cewa, tsohuwar ministar ilimi, Dr. Oby Ezekwesili, ita ce shugabar kwamitin, yayin da Farfesa Benedict Oramah, Farfesa Pat Utomi da Osita Chidoka za su taka muhimmiyar rawa wajen shirin mika mulki.
Sauran mambobin sun hada da: Uche Okafor, Farfesa Chidi Odinkalu, Steve Nworga, Ben Nwankwo, Charles Odedo, Tony Ifeanya, Ferdinand Agu, Farfesa Osita Ogbu, Chikwe Udensi, Greg Ibe da Alex Otti, da dai sauransu.
Sanarwar ta ci gaba da cewa, za a sanar da sharuddan kwamitin, da kuma yadda za a gudanar da shi a yayin kaddamar da taron farko da kuma zaman taron farko da aka shirya gudanarwa tsakanin 19 da 22 ga watan Janairu, 2022 a otal din Golden Tulip (Agulu Lake) da ke cikin Otal din Golden Tulip (Agulu Lake) jihar
Har ila yau, ya ce, a na sa ran mambobin za su isa ranar Laraba 19 ga watan Janairu, yayin da za a fara taron kaddamar da taron farko a ranar 20 ga watan Janairu.