fidelitybank

Boko Haram sun kai hari tare da yin garkuwa da jami’an ‘yan sanda

Date:

‘Yan kungiyar ta’adda ta Boko Haram sun kai farmaki makarantar horas da ‘yan sanda ta Mobile da ke karamar hukumar Limankara Gwoza a jihar Borno, inda suka yi awon gaba da mutane da dama.

Kamar yadda jaridar Punch ta rawaito, masu garkuwan sun tafi da wasu ‘yan sandan na Mobile wadanda ba a tantance adadinsu ba.

Makarantar horarwa ta na kilomita ashirin da biyar daga garin Gwoza, mahaifar Sanata Ali Ndume, shugaban kwamitin majalisar dattawa akan sojoji. Gari ne mai iyaka tsakanin Borno da karamar hukumar Madagali ta jihar Adamawa.

Rahotanni sun ce mayakan ‘yan tada kayar bayan sun kai hari makarantar horon ne a daren ranar Alhamis da manyan bindigogi inda suka rinka harbin iska kafin su yi awon gaba da jami’i mai bayar da umarni.

Harin dai na zuwa ne kwanaki bakwai, bayan da ‘yan ta’addan suka yi yunkurin kutsawa cikin sansanin sojojin Najeriya da ke Gwoza inda wasu sojojin Najeriya suka yi nasarar fatattakar su.

Kwamitin Majalisar Dattawa kan Sojoji karkashin jagorancin Sanata Ali Ndume ya kai ziyarar aiki zuwa rundunar Operation Hadin Kai da ke yankin kwanaki biyu da suka gabata.

Har ila yau, Gwamnan Jihar Borno, Babagana Zulum, ya koka da yadda matsalar tsaro a jihar da kuma yankin Arewa maso Yamma ke ciki a halin yanzu, inda ya bukaci sojoji da su daina sassauta musu.

A cewar Zulum, ‘yan ta’addan Boko Haram a yanzu suna bukukuwan aure, suna karbar haraji daga wasu al’ummomi ba tare da wata arangama da sojoji ba.

punch newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu ɗauki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta ɗaukar mataki...

Babu barazanar tsaro a Abuja – Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta ce, babu wata barazanar a babban...

Isra’ila za ta mayarwa da Iran martani duk da tsagaita wuta

Ministan tsaron Isra'ila, Katz ya bayyana cewa, ya ba...

Ba mu kai wa Isra’ila hari ba – Iran

Kafar watsa labarai ta Iran ta ruwaito gwamnatin ƙasar...

Duk da faduwar farashin mai NNPCL ya kara farashi

Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL ya ƙara farashin...

Duk wasu ƙawayen Amurka za su ɗanɗanar kuɗarsu – Iran

Rundunar dakarun juyin juya halin Iran ta fitar da...

Iran ta mayar da martani kan sojojin Amurka dake Qatar

Kafofin yaɗa labaran Iran sun bayyana cewa ƙasar ta...

Faransa ba ta goyon bayan Amurka na kifer da gwamnatin Iran – Barrot

Ministan harkokin wajen Faransa ya ce, ƙasarsu ba ta...

Kotu a Kano ta ɗaure masu satar Yara

Babbar kotun jihar Kano da ke zamanta a Miller...

Ba wata hujja da Amurka za ta kai wa Iran hari – Rasha

An gudanar da tattaunawa tsakanin shugaban Rasha Vladimir Putin...

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...
X whatsapp