fidelitybank

Gwamna mai jiran gado Soludo ya nada kwamitin rantsar da shi

Date:

Zababben gwamnan jihar Anambra, Farfesa Chukwuma Soludo, ya fitar da jerin sunayen mambobin kwamitin mika mulki mai wakilai 80 da za su taimaka wajen rantsar da shi a ranar 17 ga Maris, 2022.

A cikin wata sanarwa da ya fitar, jiya, ta hannun mai taimaka wa Soludo kan harkokin yada labarai, Joe Anatume, jerin sun kunshi mambobi 80, tare da fitattun ‘yan Najeriya, wadanda za su taka rawa daban-daban.

Ya ce, kwamitin zai tuntubi tawagar da gwamnatin jihar Anambra ta kafa, domin tabbatar da karbar mulki daga hannun gwamnatin Willie Obiano zuwa gwamnatin Soludo daga ranar 17 ga Maris, 2022.

Sanarwar ta tabbatar da cewa, tsohuwar ministar ilimi, Dr. Oby Ezekwesili, ita ce shugabar kwamitin, yayin da Farfesa Benedict Oramah, Farfesa Pat Utomi da Osita Chidoka za su taka muhimmiyar rawa wajen shirin mika mulki.

Sauran mambobin sun hada da: Uche Okafor, Farfesa Chidi Odinkalu, Steve Nworga, Ben Nwankwo, Charles Odedo, Tony Ifeanya, Ferdinand Agu, Farfesa Osita Ogbu, Chikwe Udensi, Greg Ibe da Alex Otti, da dai sauransu.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, za a sanar da sharuddan kwamitin, da kuma yadda za a gudanar da shi a yayin kaddamar da taron farko da kuma zaman taron farko da aka shirya gudanarwa tsakanin 19 da 22 ga watan Janairu, 2022 a otal din Golden Tulip (Agulu Lake) da ke cikin Otal din Golden Tulip (Agulu Lake) jihar

Har ila yau, ya ce, a na sa ran mambobin za su isa ranar Laraba 19 ga watan Janairu, yayin da za a fara taron kaddamar da taron farko a ranar 20 ga watan Janairu.

world news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na É—aukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

ÆŠanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa Æ´an Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa Æ´anbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen Æ™auyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faÉ—a ADC

Tsohon É—an jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

ÆŠan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...
X whatsapp