fidelitybank

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Date:

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga shugaban Najeriya, Bola Tinubu a gidanke da ke birnin Legas.

Cikin wani saƙo da gwamnan ya wallafa a shafinsa na X, ya ce ya kai ziyarar ne tare da ƴan’uwansa, babban yayaransa Adedeji Adeleke, da kuma ɗandan’uwansa, fitaccen mawaƙin nan David Adeleke da aka fi sani da Davido, gabanin bukukuwan babbar sallah.

Kodayake babu cikakken bayani kan abin da tattaunawar tasu ta ƙunsa, ganawar na zuwa ne kwanaki bayan Davido ya gana da Tinubu a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja, a wani abu da ake ganin tattaunawa ce tsakanin dangin Adeleke da fadar shugaban ƙasar.

A cikin watan da ya gabata ne hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta saka ranar 20 ga watan Yulin 2026 a matsayin ranar da za ta gudanar da zaɓen gwamnan jihar Osun.

Ana ganin Gwamna Adeleke – wanda ɗan jam’iyyar PDP ne – zai tsaya takara a zaɓn domin neman wa’adin mulkinsa na biyu, bayan da aka zaɓe shi a karon farko a 2022.

nigerianewstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp