Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga shugaban Najeriya, Bola Tinubu a gidanke da ke birnin Legas.
Cikin wani saƙo da gwamnan ya wallafa a shafinsa na X, ya ce ya kai ziyarar ne tare da ƴan’uwansa, babban yayaransa Adedeji Adeleke, da kuma ɗandan’uwansa, fitaccen mawaƙin nan David Adeleke da aka fi sani da Davido, gabanin bukukuwan babbar sallah.
Kodayake babu cikakken bayani kan abin da tattaunawar tasu ta ƙunsa, ganawar na zuwa ne kwanaki bayan Davido ya gana da Tinubu a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja, a wani abu da ake ganin tattaunawa ce tsakanin dangin Adeleke da fadar shugaban ƙasar.
A cikin watan da ya gabata ne hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta saka ranar 20 ga watan Yulin 2026 a matsayin ranar da za ta gudanar da zaɓen gwamnan jihar Osun.
Ana ganin Gwamna Adeleke – wanda ɗan jam’iyyar PDP ne – zai tsaya takara a zaɓn domin neman wa’adin mulkinsa na biyu, bayan da aka zaɓe shi a karon farko a 2022.