A ƙalla mutum 36 ne suka mutu wasu da dama kuma suka jikkata, sakamaon wata gobara da ta tashi a gidan yarin Burundi.
Mataimakin shugaban ƙasar, Prosper Bazombanza ya shaida wa manema labarai cewa, gobarar ta tashi ne a wani gidan yari mai cunkoso a babban birnin ƙasar Gitega, inda a ƙalla mutum 69 suka jikkata.
Hotunan da suka yaɗu a intanet sun nuna yadda ginin gidan ke ci da wuta sannan da tarin gawarwaki, waɗanda aka ce na fursunoni ne.
“Wannan babban bala’i ne,” kamar yadda wani fursuna ya shaida wa BBC ta waya.
“Zan iya cewa kusan kashi 90 cikin 100 na ɗakunan kwana sun ƙone ƙurmus.”
Wani ɗan jarida a wajen gidan yarin ya shaida wa BBC cewa ma’aikatan jinya daga asibitin Gitega sun shiga gidan yarin don taimaka wa waɗanda lamarin ya rutsa da su, yana mai cewa suna kwashe mamatan da waɗanda suka jikkata.
Gobarar ta tashi ne da misalin ƙarfe 4 na yammaci agogon ƙasar, wato ƙarfe 2 agogon GMT.