fidelitybank

Giya: Hisba ta gamu da tutsu yayin sumame

Date:

A daren ranar Talata ne wata hatsaniya ta kaure tsakanin jami’an hukumar Hisbah ta Kano da wasu matasa a wata mashayar Barasa da ke unguwar Sabon Gari a cikin garin Kano.

Rahotanni sun bayyana cewa jami’an hukumar Hisbah, sun dira a wani wajen shaye-shaye mai suna, Ballat Hughes da ke Court Road a cikin unguwar Sabon Gari.

Hukumar Hisba ta sami rahoton yadda a ke ta’ammali da Giya a wajen, domin kwace Barasa da sauran kayan shaye-shaye.

Lamarin da ya fusata matasan da ke wajen har ta kai ga sun fara jifan ‘yan Hisbah tare da fasa kwalaben giya, wanda ya kai ga samun hatsaniya a wajen.

Shaidun gani da ido sun tabbatar da cewa bayan faruwar lamarin, ‘yan daba da wasu bata gari sun yi amfani da wannan damar inda suka sace wasu muhimman kayayyaki a wajen.

Wannan lamarin ne ya sanya, shugaban hukumar Hisba, Muhammad Harun Ibn Sina, ya magantu, ya ce”Mun samu rahoton faruwar cewa a na tara mata da matasa a na koya musu shan Giya da kwaya a wajen, hakan ne ya sa mu ka kai sumame wajen, amma mun sami nasarar taho da mai siyar da Giyar a wajen, bayan an jefe mu da duwatsu, har da raunata jam’ian mu, kuma za mu gurfanar da mai siyar da Giyar a gaban kotu, domin ta girbi abin da ta shuka”. Inji Ibn Sina.

www.legit news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp