Akalla mutum 26 ne aka tabbatar da mutuwar su a gida daya, sakamakon wata girgizar kasa mai karfin mataki 5.3 a kasar Afghanistan.
Mutanen sun gamu da ajalinsu ne bayan rufin gidansu ya rufta a kansu a yankin Qadis da ke Yammacin Lardin Badghis na kasar.
A cewar mai magana da yawun Lardin Badghis, Baz Mohammad Sarwary.“Matan aure biyar da kananan yara hudu na daga cikin mutum 26 da suka rasu a girgizar kasar,”
Ya ce, girgizar kasar ta kuma lalata wasu gidaje a gundumar Muqr da ke cikin Lardin, sai dai ba a kai ga samun alkaluman wadanda lamarin ya shafa a yankin ba tukuna.
Yankin Qadis dai na daga cikin yankunan da matsalar karancin ruwan sama ta fi yi wa illa a kasar Afhganistan, kuma ta yi ta fama da rashin kayan agaji daga kasashen duniya a tsawon shekara 20 da suka gabata.
Kasar Afghanistan dai na yawan fama da girgizar kasa, musamman a yankin da Tsaunin Hindu Kush yake, wanda ke kan iyakokin kasar da nahiyar Turai da kuma Asiya ta bangaren Indiya.