Rundunar hadin gwiwa ta ‘yan banga da mafarauta ta dakile kai wani harin garkuwa da matafiya a gadar Ahoko, da ke kan babbar hanyar Abuja zuwa Lokoja.
Guda daga cikin mamba na ‘yan bangar wanda ya nemi a sakaye sunansa, ya ce an kama mutanen biyu da ake zargi da yin garkuwa.
Ya ce masu garkuwa da mutanen sun yi wa matafiya kwanton bauna ne a wata lankwasa kusa da gadar a lokacin da tawagar ‘yan banga da mafarauta suka isa wurin.
Dan banga din ya ce an mika masu garkuwa da mutanen biyu ga jami’an tsaro a Lokoja, babban birnin jihar Kogi, tare da bindigu biyu da aka kwato daga hannun masu garkuwar.
Kwamandan kungiyar mafarautan na jihar Kogi, Hassan Yakubu, ya tabbatar da kama mutanen biyu a Ahoko, inda ya ce an mika su ga jami’an tsaro. Inji Aminiya.