fidelitybank

Ganduje ya sanya sunan Bashir Tofa a jami’ar Wudil – KCSF

Date:

Gamayyar ƙungiyoyin fararen hula a jihar Kano (KCSF), sun buƙaci gwamnan jihar, Dr Abdullahi Umar Ganduje da ya sauya sunan jami’ar Kimiyya da Fasaha mallakin jihar da ke garin Wudil, zuwa sunan marigayi Alhaji Bashir Othman Tofa.

A cikin wata sanarwa ta’aziyya da KCSF ta aike waGanduje, mai ɗauke da sa hannun shugaban kungiyar, Kwamared Ibrahim Waya da Sakataren ta, Peter Hassan Tijjani.

A cikin sakon ta’aziyyar, wacce jami’in yaɗa labarai na KCSF ɗin Kwamared MK Adam Rano ya rabawa manema labarai a Kano, sun bayyana marigayi Alhaji Bashir Othman Tofa a matsayin ɗan kishin ƙasa da ya taka muhimmiyar rawa wajen cigaban jihar Kano da ma Arewacin Najeriya bki daya.

Haka kuma sanarwar ta ƙara da cewa, Alhaji Bashir Tofa, ya rasu a dai-dai lokacin da ya ke tsaka da bayar da gudunmawar sa wajen cigaban al’umma ta hanyar taimaka musu a kan abubuwan da su ka addabe su tare da da ganin an samu hadin kai tsakanin ƴan Najeriya.

Hakazalika KCSF ta ƙara da cewa mutuwar Bashir Tofa ta haifar da wani babban giɓi da zai wahalar cikewa a nan kusa, musamman idan a ka yi la’akari da dattaku da ayyukan alkhairi da ya ke yi a lokacin rayuwarsa.

Alhaji Bashir Othman Tofa ya na daga cikin dattijan da su ka yi ta fafutukar ganin Arewacin Najeriya ya fita daga matsalolin tsaron da ya fada a ciki.

Haka kuma tarihin siyasar Najeriya ba zai taba cika ba, ba tare da an ambato Alhaji Bashir Usman Tofa, musamman kan abin da ya faru a shekarar 1993 lokacin zaɓen shugaban kasa.

 

vgn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Luis Diaz ya zaba wa kansa makoma da ya bar Liverpool – James

Kyaftin din Colombia, James Rodríguez, ya dage cewa dan...

Ka fito ka baiwa Matawalle hakuri ko ka fuskanci fushin kotu – Shinkafi

Wani mai fafutukar kare hakkin bil’adama, Dakta Suleiman Shuaibu...

Liverpool za su sayar da ‘yan wasa uku su dauki Isak

Liverpool a shirye take ta sayar da matasan yan...

Ba zamu daga wa Hamas kafa ba har sai an saki mutanen mu – Netanyahu

Firaiministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, ya yi dogon...

Za mu gyara tsarin Maiduguri saboda ambaliya – Zulum

Gwamnan jihar Borno Babagana Umara Zulum ya ce, gwamnatinsa...

Dubban mutane sun yi zanga-zangar goyon bayan Falasɗinawa a Australia

Dubban mutane ne suka gudanar da zanga-zangar goyon bayan...

Mata da kanan Yara ne Ambaliya ta daidaita a jihohi 19 – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa, NEMA, ta...

Facebook ya ƙi amincewa da tsare-tsaren Turai na amfani da AI

Wasu muhimman tsare-tsare na dokokin Tarayyar Turai kan amfani...

Ranar 18 za a fara rajistar zabe – INEC

Hukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC ta sanar da...

Trump ya tura jiragen ruwa na yaki masu dauke da makaman nukiliya kusa da Rasha

Shugaba Trump ya ce, ya umarci a matsar da...

Amnesty na tuhumar gwamnatin Najeriya kan bacewar Dadiyata

Ƙungiyar Amnesty International ta yi Allah-wadai da sakacin da...

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...
X whatsapp