Gamayyar ƙungiyoyin fararen hula a jihar Kano (KCSF), sun buƙaci gwamnan jihar, Dr Abdullahi Umar Ganduje da ya sauya sunan jami’ar Kimiyya da Fasaha mallakin jihar da ke garin Wudil, zuwa sunan marigayi Alhaji Bashir Othman Tofa.
A cikin wata sanarwa ta’aziyya da KCSF ta aike waGanduje, mai ɗauke da sa hannun shugaban kungiyar, Kwamared Ibrahim Waya da Sakataren ta, Peter Hassan Tijjani.
A cikin sakon ta’aziyyar, wacce jami’in yaɗa labarai na KCSF ɗin Kwamared MK Adam Rano ya rabawa manema labarai a Kano, sun bayyana marigayi Alhaji Bashir Othman Tofa a matsayin ɗan kishin ƙasa da ya taka muhimmiyar rawa wajen cigaban jihar Kano da ma Arewacin Najeriya bki daya.
Haka kuma sanarwar ta ƙara da cewa, Alhaji Bashir Tofa, ya rasu a dai-dai lokacin da ya ke tsaka da bayar da gudunmawar sa wajen cigaban al’umma ta hanyar taimaka musu a kan abubuwan da su ka addabe su tare da da ganin an samu hadin kai tsakanin ƴan Najeriya.
Hakazalika KCSF ta ƙara da cewa mutuwar Bashir Tofa ta haifar da wani babban giɓi da zai wahalar cikewa a nan kusa, musamman idan a ka yi la’akari da dattaku da ayyukan alkhairi da ya ke yi a lokacin rayuwarsa.
Alhaji Bashir Othman Tofa ya na daga cikin dattijan da su ka yi ta fafutukar ganin Arewacin Najeriya ya fita daga matsalolin tsaron da ya fada a ciki.
Haka kuma tarihin siyasar Najeriya ba zai taba cika ba, ba tare da an ambato Alhaji Bashir Usman Tofa, musamman kan abin da ya faru a shekarar 1993 lokacin zaɓen shugaban kasa.