fidelitybank

Ganduje ya sanya sunan Bashir Tofa a jami’ar Wudil – KCSF

Date:

Gamayyar ƙungiyoyin fararen hula a jihar Kano (KCSF), sun buƙaci gwamnan jihar, Dr Abdullahi Umar Ganduje da ya sauya sunan jami’ar Kimiyya da Fasaha mallakin jihar da ke garin Wudil, zuwa sunan marigayi Alhaji Bashir Othman Tofa.

A cikin wata sanarwa ta’aziyya da KCSF ta aike waGanduje, mai ɗauke da sa hannun shugaban kungiyar, Kwamared Ibrahim Waya da Sakataren ta, Peter Hassan Tijjani.

A cikin sakon ta’aziyyar, wacce jami’in yaɗa labarai na KCSF ɗin Kwamared MK Adam Rano ya rabawa manema labarai a Kano, sun bayyana marigayi Alhaji Bashir Othman Tofa a matsayin ɗan kishin ƙasa da ya taka muhimmiyar rawa wajen cigaban jihar Kano da ma Arewacin Najeriya bki daya.

Haka kuma sanarwar ta ƙara da cewa, Alhaji Bashir Tofa, ya rasu a dai-dai lokacin da ya ke tsaka da bayar da gudunmawar sa wajen cigaban al’umma ta hanyar taimaka musu a kan abubuwan da su ka addabe su tare da da ganin an samu hadin kai tsakanin ƴan Najeriya.

Hakazalika KCSF ta ƙara da cewa mutuwar Bashir Tofa ta haifar da wani babban giɓi da zai wahalar cikewa a nan kusa, musamman idan a ka yi la’akari da dattaku da ayyukan alkhairi da ya ke yi a lokacin rayuwarsa.

Alhaji Bashir Othman Tofa ya na daga cikin dattijan da su ka yi ta fafutukar ganin Arewacin Najeriya ya fita daga matsalolin tsaron da ya fada a ciki.

Haka kuma tarihin siyasar Najeriya ba zai taba cika ba, ba tare da an ambato Alhaji Bashir Usman Tofa, musamman kan abin da ya faru a shekarar 1993 lokacin zaɓen shugaban kasa.

 

nigeria legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp