fidelitybank

Ganduje ya jinjinawa hukumar alhazai ta kasa NAHCON

Date:

Gwamnan jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya yabawa shugaban hukumar alhazai ta kasa (NAHCON), Alhaji Zikrullah Kunle Hassan, bisa irin ayyukan da hukumar ta ke yi.

Gwamna Ganduje ya yabawa Alhaji Hassan a ziyarar da ya kai shelkwatar NAHCON da ke Abuja, a ranar Laraba.

Gwamnan ya ce, daya daga cikin tsare-tsaren da ya dace a yaba masa shi ne shirin ceton aikin Hajji (HSS), wanda aka tsara don taimakawa masu karamin karfi da sauran su wajen biyan kudi a hankali don samun damar zuwa aikin Hajji.

Ya ce, tun farko jihar Kano ta rungumi shirin, dalilin da ya sa aka samar da yanayi mai kyau don samun nasarar ta a jihar.

Gwamnan ya tunatar da Alhaji Hassan cewa, aikin ginin otal ya tsaya, lamarin da ka iya janyo karin farashi sakamakon hauhawar farashin kayayyakin gini a kodayaushe.

Ya yi kira da a dauki matakin gaggawa kan lamarin, yayin da Gwamna Ganduje ya bukaci a kara wa jiharsa gurbin aikin hajji idan akwai.

Da yake karbar gwamnan hedikwatar NAHCON, Alhaji Hassan ya bayyana ziyarar Gwamna Ganduje a matsayin mai tarihi.

Ya bayyana cewa gwamnan shi ne ya fi kowa goyon bayan HSS sannan ya bayyana gwamnan a matsayin mai karbar shugabancin NAHCON.

Shugaban NAHCON ya ce jihar Kano ce jiha ta farko da hukumar ta fara gudanar da shirin hadin gwiwar jama’a masu zaman kansu cikin nasara tare da godewa gwamnan bisa nasarar shirin.

Alhaji Hassan ya kuma bayyana Kano a matsayin mai muhimmanci ga hukumar NAHCON, inda ya yi alkawarin taimakawa Kano da bukatunta saboda mutunta jihar.

Dangane da dakatar da ginin otal din kuwa, shugaban NAHCON ya dora laifin rashin kudi da aka yi.

nhgsfp

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamna Zulum ya musanta shirin sauya sheƙa zuwa ADC

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno ya musanta...

Tinubu ta ceci Najeriya faÉ—a wa cikin mawuyacin hali – Ribadu

Mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan tsaro, Malam...

Isra’ila za ta aika tawaga Qatar don tattaunawa da Hamas

Isra’ila ta yanke shawarar aika wata tawaga zuwa Qatar...

Jagoran Iran ya bayyana gaban jama’a karon farko tun soma yaÆ™i da Isra’ila

Jagoran addini na Iran Ayatollah Ali Khamenei ya bayyana...

Muna aiki tukuru don bunÆ™asa noma a Najeriya – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu na Najeriya ya tabbatar da cewa...

Duk wanda ya yi sata idan na zama shugaban Æ™asa sai na yake shi – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya, Atiku Abubakar ya yi alwashin...

Ina nan a PDP na ban gudu ba – Adeleke

Gwamnan jihar Osun, ya musanta rahotonnin da ke cewa...

Tinubu ya isa birnin Rio na Brazil don halartar taron BRICS

Shugaban kasa Bola Tinubu ya isa birnin Rio de...

Matakan da muke É—auka kan kisan matafiya a Plateau – Mutfwang

Gwamna Caleb Mutfwang na jihar Filato, ya ce gwamnatinsa...

Tinubu ya gaji tattalin arziki da ya kusa durkushewa – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyeson Wike, ya ce...

Har yanzu PDP tana nan da Æ™arfinta – Isa Ashiru

Yayin da fagen siyasar Najeriya ke ci gaba da...

An kama ɗan shekara 70 kan zargin kashe ƙanwarsa a Jigawa

Rundunar Æ´ansandan jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya ta...
X whatsapp