Jam’iyar APC, ɓangaren Sanata Ibrahim Shekarau ta ce tsohon gwamnan bai tuntuɓi kowa a cikin ƴan ɓangaren na sa ba lokacin da ya je ya gana da Bola Ahmed Tinubu, Jagoran APC na ƙasa.
Wani ɗan ɓangaren na Shekarau, wanda ya nemi kar a faɗi sunan sa ne ya shaidawa Jaridar Daily Trust.
Sannan kuma ɗan ɓangaren na Shekarau ya yi ƙorafin cewa har yanzu Sanatan bai baiyana musu abinda su ka tattauna da Tinubu tun bayan da ya dawo Kano.
“Mu abinda mu ke gani, ganawar ta kashin kansa ce ba wai domin ƴan bangaren namu ba saboda ya tafi ba tare da izinin mu ba, kuma tun bayan dawowarsa, bai baiyana mana abinda su ka tattauna ba.
“Abin da na ke so na gaya maka shine ba wanda ya isa ya yi mana kama-karya a Kano a 2023. Kano ta fi ƙarfin kowa,” in ji shi.