fidelitybank

Fastocin Orji Kalu na takarar shugaban kasa sun karade Bauchi

Date:

Hotunan tsohon gwamnan jihar Abia, Orji Uzor Kalu na takarar shugaban kasa sun karade jihar Bauchi.

Wata kungiyar goyon bayan siyasa ta Kalu domin neman ya tsaya takarar shugaban kasa a 2023 ta manna fastocin Sanata Orji Uzor Kalu a manyan tituna da bangwayen gidaje a jihar.

Lamarin dai na zuwa ne makonni kadan bayan da wasu matasan Arewa suka kai Kalu gaban wata babbar kotun jihar Bauchi inda suka bukaci kotun ta tilasta masa tsayawa takarar shugaban kasa a 2023.

Mazauna babban birnin jihar Bauchi sun wayi gari da ganin fastocin Kalu a ko’ina tare da nuna goyon bayansu ga Kalu a mtsayin shugaban Najeriya a 2023, wanda ya kau da kai wanda zai iya hada kan kasar da kuma ceto kasar daga tarwatsewar da ke kusa.

An hango fastocin a fadar Sarkin Bauchi da kewaye, babbar kasuwa, Awalah, hukumar kashe gobara, titin Jos da wasu hanyoyi da gidaje da dama.

Wasu daga cikin Fastocin Kalu da suka karade Bauchi.

Kungiyar ta kira Kalu a matsayin mafi kyawu a takarar shugaban kasa a 2023, inda ta bukace shi da ya tsaya takara a jam’iyyar APC.

Jikin shatale-tale a jihar Bauchi manne da hotun Kalu.

Kungiyar ta bukaci jam’iyyar APC da ta fara shirin daukar Kalu a matsayin dan takara daya tilo a jam’iyyar, saboda kwarewarsa na gudanar da mulki da gogewarsa da kuma kira ga kasa wanda ta ce shi ne ya fi dacewa ya mulki Najeriya a 2023.

jalingo news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuÉ—in gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuÉ—in gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuÉ—a

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiÉ—a wa Isra'ila wasu...
X whatsapp