Hotunan tsohon gwamnan jihar Abia, Orji Uzor Kalu na takarar shugaban kasa sun karade jihar Bauchi.
Wata kungiyar goyon bayan siyasa ta Kalu domin neman ya tsaya takarar shugaban kasa a 2023 ta manna fastocin Sanata Orji Uzor Kalu a manyan tituna da bangwayen gidaje a jihar.
Lamarin dai na zuwa ne makonni kadan bayan da wasu matasan Arewa suka kai Kalu gaban wata babbar kotun jihar Bauchi inda suka bukaci kotun ta tilasta masa tsayawa takarar shugaban kasa a 2023.
Mazauna babban birnin jihar Bauchi sun wayi gari da ganin fastocin Kalu a ko’ina tare da nuna goyon bayansu ga Kalu a mtsayin shugaban Najeriya a 2023, wanda ya kau da kai wanda zai iya hada kan kasar da kuma ceto kasar daga tarwatsewar da ke kusa.
An hango fastocin a fadar Sarkin Bauchi da kewaye, babbar kasuwa, Awalah, hukumar kashe gobara, titin Jos da wasu hanyoyi da gidaje da dama.

Kungiyar ta kira Kalu a matsayin mafi kyawu a takarar shugaban kasa a 2023, inda ta bukace shi da ya tsaya takara a jam’iyyar APC.

Kungiyar ta bukaci jam’iyyar APC da ta fara shirin daukar Kalu a matsayin dan takara daya tilo a jam’iyyar, saboda kwarewarsa na gudanar da mulki da gogewarsa da kuma kira ga kasa wanda ta ce shi ne ya fi dacewa ya mulki Najeriya a 2023.