fidelitybank

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Date:

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta sake rage farashin shinkafa da sauran kayan abinci, wanda ya ce tun shekarar da ta gabata yake ta sauka.

Abdul Samad Rabiu ya bayyana haka ne ranar Alhamis jim kaɗan bayan ganawarsa ta Tinubu a fadar shugaban ƙasar.

Shugaban na BUA ya yaba wa Tinubu kan bayara da damar shigo da wasu kayan abinci da ya yi, yana mai bayyana matakin da ‘kyakkyawa” da ya ce ya taimaka wajen karyewar farashin kayan abinci a ƙasar.

A watan Yulin 2024 ne gwamnatin Shugaba Tinubu ta bayayna dakatar da karɓar kudin fito na shigo da kayan abinci a wani mataki na magance hauwarar farashin kayayyaki.

BUA ya zargi masu sayen kayyaki domin ɓoyewa da haddasa tashin farashin.

Ya ce da zarar lokacin girbe amfanin gona ya yi, sai wasu su riƙa sayen kayan suna ɓoyewa, har tsawo wata uku, daga baya kuma su fito da kayan su tsawwala farashi domin sayarwa kamfanonin sarrafa abinci .

To sai dai ya ce bayan matakin shugaban ƙasar, kamfanonin sarrrafa shinkafa sun shigo da wadataccen kaya, lamarin da ya sa dole masu ɓoye kayan suka fito da nasu suna sayarwa a farashi mai sauƙi.

”Wannan shi ne abin muka yi, kuma za mu ci gaba da yin haka domin mara wa matakin gwamnati baya na tabbatar da farashin abinci ya sauka, kuma na tabbata farashin zai ci gaba da sauka”.

Kalaman BUA na zuwa ne a daidai lokacin da rahoton hukumar Ƙididdiga na ƙasa NBS ke nuna cewa an samu raguwar farashin kayyaki a ƙasar a watan Afilu idan aka kwatanta da watan Maris da ya gabata.

sun news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...

Tinubu ya haramta fitar da ɗanyen man kaɗanya

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bayar da umarnin dakatar...

Hisba ta karɓi ƙorafe-ƙorafe 83,776 a Kano

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta bayyana cewa, a...

Ganduje ba dan cin hanci ba ne – Martanin Garba Ga Gwamnatin Kano

Tsohon kwamishinan yaɗa labarai na Jihar Kano, Muhammad Garba,...

Kungiyar Malaman Jami’o’i bangaren BUK sun yi zanga-zangar Lumana

Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU), reshen Jami’ar Bayero Kano (BUK),...
X whatsapp