fidelitybank

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Date:

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta sake rage farashin shinkafa da sauran kayan abinci, wanda ya ce tun shekarar da ta gabata yake ta sauka.

Abdul Samad Rabiu ya bayyana haka ne ranar Alhamis jim kaɗan bayan ganawarsa ta Tinubu a fadar shugaban ƙasar.

Shugaban na BUA ya yaba wa Tinubu kan bayara da damar shigo da wasu kayan abinci da ya yi, yana mai bayyana matakin da ‘kyakkyawa” da ya ce ya taimaka wajen karyewar farashin kayan abinci a ƙasar.

A watan Yulin 2024 ne gwamnatin Shugaba Tinubu ta bayayna dakatar da karɓar kudin fito na shigo da kayan abinci a wani mataki na magance hauwarar farashin kayayyaki.

BUA ya zargi masu sayen kayyaki domin ɓoyewa da haddasa tashin farashin.

Ya ce da zarar lokacin girbe amfanin gona ya yi, sai wasu su riƙa sayen kayan suna ɓoyewa, har tsawo wata uku, daga baya kuma su fito da kayan su tsawwala farashi domin sayarwa kamfanonin sarrafa abinci .

To sai dai ya ce bayan matakin shugaban ƙasar, kamfanonin sarrrafa shinkafa sun shigo da wadataccen kaya, lamarin da ya sa dole masu ɓoye kayan suka fito da nasu suna sayarwa a farashi mai sauƙi.

”Wannan shi ne abin muka yi, kuma za mu ci gaba da yin haka domin mara wa matakin gwamnati baya na tabbatar da farashin abinci ya sauka, kuma na tabbata farashin zai ci gaba da sauka”.

Kalaman BUA na zuwa ne a daidai lokacin da rahoton hukumar Ƙididdiga na ƙasa NBS ke nuna cewa an samu raguwar farashin kayyaki a ƙasar a watan Afilu idan aka kwatanta da watan Maris da ya gabata.

nigeria news today 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp