fidelitybank

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Date:

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta sake rage farashin shinkafa da sauran kayan abinci, wanda ya ce tun shekarar da ta gabata yake ta sauka.

Abdul Samad Rabiu ya bayyana haka ne ranar Alhamis jim kaɗan bayan ganawarsa ta Tinubu a fadar shugaban ƙasar.

Shugaban na BUA ya yaba wa Tinubu kan bayara da damar shigo da wasu kayan abinci da ya yi, yana mai bayyana matakin da ‘kyakkyawa” da ya ce ya taimaka wajen karyewar farashin kayan abinci a ƙasar.

A watan Yulin 2024 ne gwamnatin Shugaba Tinubu ta bayayna dakatar da karɓar kudin fito na shigo da kayan abinci a wani mataki na magance hauwarar farashin kayayyaki.

BUA ya zargi masu sayen kayyaki domin ɓoyewa da haddasa tashin farashin.

Ya ce da zarar lokacin girbe amfanin gona ya yi, sai wasu su riƙa sayen kayan suna ɓoyewa, har tsawo wata uku, daga baya kuma su fito da kayan su tsawwala farashi domin sayarwa kamfanonin sarrafa abinci .

To sai dai ya ce bayan matakin shugaban ƙasar, kamfanonin sarrrafa shinkafa sun shigo da wadataccen kaya, lamarin da ya sa dole masu ɓoye kayan suka fito da nasu suna sayarwa a farashi mai sauƙi.

”Wannan shi ne abin muka yi, kuma za mu ci gaba da yin haka domin mara wa matakin gwamnati baya na tabbatar da farashin abinci ya sauka, kuma na tabbata farashin zai ci gaba da sauka”.

Kalaman BUA na zuwa ne a daidai lokacin da rahoton hukumar Ƙididdiga na ƙasa NBS ke nuna cewa an samu raguwar farashin kayyaki a ƙasar a watan Afilu idan aka kwatanta da watan Maris da ya gabata.

nigeria peace corps

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...
X whatsapp