Mahukunta a kasar Farasansa sun bayar da umarnin rufe wani masallaci har na tsawon watanni 6, sakamakon zargin tunzura mutane.
Ministan harkokin cikin gida na kasar Faransa, Gerald Darmanin ne ya sanar da hakan cewa umarnin ya buiyo bayan masallacin na gudanar da hudubar sa a kan Yahudawa da mabiya addinin kirista da dai sauran su.
Sai dai kuma lauyan masallacin Samim Bolaky a zantawansa da kamfanin dillancin labarai na AFP cewa zasu daukaka kara a kotun yankin Amiens bisa wannan umarnin .
Masallacin da ke arewacin kasar Faransa an dai rufe shi ne har na tsawon wattanni 6
A kalla masallatai 25 kasar Faransa ta rufe tun daga watan Agusta har kawo wannan lokaci. Wanda adadin masallatan da aka rufe kawo yanzu a kasar Faransa an rufe masallatai 21 daga cikin 99 6 daga ciki ana kan hanyar rufe su.
A kalla dai musulmai 2,620 ne ke gudanar da addinin musulnci a kasar ta faransa kamar yadda kamfanin dilancin labarai na AFP ya rawaito.