fidelitybank

Fadar shugaban ƙasa ta tabbatar da murabus ɗin ƙaramin ministan albarkatun man fetur

Date:

Fadar Shugaban kasa ta tabbatar da murabus din Karamin Ministan Albarkatun Man Fetur, Cif Timipre Sylva, gabanin zaben fitar da gwani na jam’iyyar APC a jihar Bayelsa a wata mai zuwa.

A ranar Juma’a, a wani sako da ya wallafa a shafinsa na Twitter, Bashir Ahmad, mai taimaka wa shugaban kasa Muhammadu Buhari kan harkokin sadarwa na zamani, ya tabbatar da faruwar lamarin.

“Ministan albarkatun man fetur, kuma tsohon gwamnan jihar Bayelsa, H.E. Timipre Sylva, ya yi murabus daga mukaminsa don tsayawa takara a zaben gwamnan Bayelsa mai zuwa,” Ahmad ya wallafa a shafinsa na Twitter.

Sanarwar ta yi karin haske kan rade-radin da ke tattare da murabus din Ministan.

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, INEC, ta tsayar da ranar 11 ga watan Nuwamba, 2023, domin gudanar da zaben gwamna a jihohin Bayelsa, Kogi da kuma Imo.

Maris 27 tsakanin Afrilu 17, 2023, an tsara ranakun da za a gudanar da zaɓen fidda gwani na jam’iyyun siyasa.

nigeria newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...
X whatsapp