Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa, Adams Oshiomhole, ya yi ikirarin cewa babban bankin Najeriya, CBN ya yaudari shugaban kasa Muhammadu Buhari da sake fasalin kudin Naira.
Oshiomhole, wanda ke magana a gidan Talabijin na Channels mai suna ‘The 2023 Verdict’ da aka watsa a ranar Lahadi, ya yi ikirarin cewa manufar na da nufin murde zaben shugaban kasa na wannan watan.
Sai dai tsohon gwamnan jihar Edo ya wanke Buhari daga duk wani laifi.
Karanta Wannan: Ina goyon bayan CBN na sauya kudi – Ben Bruce
A cewarsa, CBN ya sayar wa Buhari wani dalili na yaki da cin hanci da rashawa, wanda ya sanya shugaban kasar ya amince da wannan manufa.
“Zan iya tsammani – ban kasance a wurin ba – domin samun amincewar, na yi imanin cewa CBN ta yaudari Shugaban kasa ta hanyar kara wajabcin gudanar da zabe ba tare da cin hanci da rashawa ba kamar zabe shi ne kadai aikin da wannan shugaban ke da alhakinsa.
“Shugaba Buhari da na sani ba zai sha wahala wajen amincewa ba,” in ji Oshiomhole.