Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir Ahmad El-Rufai, ya halarci sallar jana’izar ɗan majalisar dokokin jihar Kaduna, Rilwan Aminu Gadagau da ‘yan ta’adda su ka kashe shi.
‘Yan ta’adda sun harbe Rilwan Aminu Gadagau wanda ke wakiltar mazabar Giwa ta yamma ne a kan hanyar Kaduna zuwa Zariya a ranar Litinin.
A wata sanarwa da kwamishinan tsaro na cikin gida da harkokin cikin gida na jihar Kaduna Samuel Aruwan ya fitar, ta ce kakakin majalisar dokokin jihar Kaduna, Yusuf Ibrahim Zailani da kuma masallatan Juma’a na Haruna Danja da ke Tudun Wada a garin Zaria sun tarbi gwamnan.
El-Rufa’I, ya kuma yi addu’ar Allah ya jikan sa, da kuma rayukan sauran ‘yan kasar da suka rasa rayukansu a hare-haren baya-bayan nan da aka kai a jihar.