fidelitybank

EFCC ta titsiye dakataciyar babbar jami’ar hukumar NSIP

Date:

Bayanai sun ce hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta EFCC na ci gaba da binciken shugabar hukumar ba da tallafin dogaro da kai ta Najeriya, wato Social Investment Programme – da aka dakatar.

A jiya Talata ne jami’an hukumar suka dira a ofishin Hajiya Halima Shehu tare da gudanar da bincike, daga bisani kuma ta isa ofishin EFCC, inda suka yi mata tambayoyi har cikin dare.

Shugaba Tinubu ne ya dakatar da ita daga muƙamin babbar jami’ar hukumar NSIPA wata uku kacal bayan naɗa ta, da kuma tabbatar da ita a cikin watan Oktoba.

A baya ta taɓa aiki da ma’aikatar jin ƙai ta tarayya daga 2017 zuwa 2022.

Rahotanni sun ce shugabar ta NSIPA da aka dakatar na shirin gudanar da taron manema labarai ne a ranar Talata, lokacin da jami’ai daga hukumar EFCC suka je ofishinta a birnin Abuja.

Jaridar Punch ta ambato wata majiya na cewa an samu rashin jituwa tsakanin Halima Shehu da ministar jin ƙai ta yanzu, Dr. Betta Audu tun lokacin da ta kama aiki saboda zargin cewa ziƙau ita kaɗai tana yin amfani da kuɗaɗen hukumar waɗanda aka tanada don bayar da tallafi ga ƙungiyoyin jama’a masu rauni.

An kafa shirin ba da ƙwarewar dogaro da kai ne don tallafa wa miliyoyin ‘yan Najeriya su fita daga cikin talauci da inganta harkokin cuɗanyar al’umma da kuma samar da sana’o’i ga talakawa da ‘yan ƙasa masu rauni.

Hukumar ce kuma ke da alhakin kula da shirye-shiryen yaƙi da talauci kamar shirin ciyar da ɗalibai ‘yan makaranta na ƙasa.

An ambato Halima Shehu a baya-bayan nan yayin wani taron manema labarai a Abuja, tana jaddada ƙudurinta na tabbatar da gaskiya wajen aiwatar da shirin ba da tallafin kuɗi dala miliyan 800 na Bankin Duniya.

legitnews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp